< Deuteronomy 11 >

1 Therefore love the Lord thy God and observe his precepts and ceremonies, his judgments and commandments at all times.
To, sai ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kullum ku kuma kiyaye abubuwan da yake bukata, ku kiyaye ƙa’idodinsa, dokokinsa da kuma umarnansu.
2 Know this day the things that your children know not, who saw not the chastisements of the Lord your God. his great doings and strong hand, and stretched out arm,
Ku tuna a yau, cewa’ya’yanku ba su ne suka gani suka kuma ɗanɗana horon Ubangiji Allahnku ba; ba su suka gani girmansa, hannunsa mai ƙarfi, hannunsa mai iko;
3 The signs and works which he did in the midst of Egypt to king Pharao, and to all his land,
alamun da ya aikata da abubuwan da ya yi a cikin Masar, ga Fir’auna sarkin Masar da kuma ga dukan ƙasarsa ba;
4 And to all the host of the Egyptians, and to their horses and chariots: how the waters of the Red Sea covered them, when they pursued you, and how the Lord destroyed them until this present day:
ba su suka gani abin da ya yi wa mayaƙan Masar, da dawakansu da keken yaƙinsu, yadda ya sha kansu da ruwan Jan Teku yayinda suke bin ku, da yadda Ubangiji ya hallaka su ƙaƙaf ba.
5 And what he hath done to you in the wilderness, till you came to this place:
Ba’ya’yanku ba ne suka gani abin da ya yi dominku a hamada har sai da kuka kai wannan wuri ba,
6 And to Dathan and Abiron the sons of Eliab, who was the son of Ruben: whom the earth, opening her mouth swallowed up with their households and tents, and all their substance, which they had in the midst of Israel.
ba su ba ne suka gani abin da ya yi ga Datan da Abiram,’ya’yan Eliyab mutumin Ruben, sa’ad da ƙasa ta buɗe bakinta a tsakiyar dukan Isra’ila ta haɗiye su tare da gidajensu, tentunansu da kowane abu mai rai da yake nasu ba.
7 Your eyes have seen all the greet works of the Lord, that he hath done,
Amma idanunku ne suka ga dukan waɗannan manyan abubuwan da Ubangiji ya yi.
8 That you may keep all his commandments, which I command you this day, and may go in, and possess the land, to which you are entering,
Saboda haka sai ku kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, don ku sami ƙarfin da za ku shiga, ku kuma karɓi ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaka,
9 And may live in it a long time: which the Lord promised by oath to your fathers, and to their seed, a land which floweth with milk and honey.
domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninku zai ba su da zuriyarsu, ƙasa mai zub da madara da zuma.
10 For the land, which thou goest to possess, is not like the land of Egypt, from whence thou camest out, where, when the seed is sown, waters are brought in to water it after the manner of gardens.
Ƙasar da kuke shiga, ku karɓa, ba kamar ƙasar Masar ba ce, inda kuka fito, inda kuka shuka iri, ku yi ta zuwa kuna banruwa kamar lambu.
11 But it is a land of hills and plains, expecting rain from heaven.
Amma ƙasar da kuke haye Urdun ku mallaki, ƙasa ce ta duwatsu da kwaruruka wadda ruwan sama ne yake jiƙe ta.
12 And the Lord thy God doth always visit it, and his eyes are on it from the beginning of the year unto the end thereof.
Ƙasa ce da Ubangiji Allahnku yake lura da ita; idanun Ubangiji Allahnku yana a kai daga farkon shekara har zuwa ƙarshenta.
13 If then you obey my commandments, which I command you this day, that you love the Lord your God, and serve him with all your heart, and with all your soul:
Saboda haka in kun yi biyayya ga umarnan da nake ba ku a yau cikin aminci, kuna ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kuna kuma bauta masa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku,
14 He will give to your land the early rain and the latter rain, that you may gather in your corn, and your wine, and your oil,
sai in aika da ruwan sama a ƙasarku a lokacinsa, ruwan saman bazara da kuma na kaka, don ku tattara hatsinku, sabon inabinku da kuma manku.
15 And your hay out of the fields to feed your cattle, and that you may eat and be filled.
Zan tanadar da ciyawa a filaye don shanunku, za ku ci, ku kuma ƙoshi.
16 Beware lest perhaps your heart be deceived, and you depart from the Lord, and serve strange gods, and adore them:
Ku yi hankali, kada a ruɗe ku har ku bauta wa alloli, ku kuma yi musu sujada,
17 And the Lord being angry shut up heaven, that the rain come not down, nor the earth yield her fruit, and you perish quickly from the excellent land, which the Lord will give you.
don kada fushin Ubangiji yă ƙuna a kanku, yă rufe sammai, ku rasa ruwa, ƙasa kuma ta kāsa ba da amfaninta, da haka za ku murmutu nan da nan a kyakkyawar ƙasar da Ubangiji yake ba ku.
18 Lay up these my words in your hearts and minds, and hang them for a sign on your hands, and place them between your eyes.
Saboda haka, sai ku riƙe waɗannan kalmomina gam a zukatanku da ranku; ku ɗaura su kamar alama a hannuwanku, da goshinku.
19 Teach your children that they meditate on them, when thou sittest in thy house, and when thou walkest on the way, and when thou liest down and risest up.
Ku koyar da su ga’ya’yanku, ku yi ta haddace su, sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
20 Thou shalt write them upon the posts and the doors of thy house:
Ku rubuta su a kan madogaran ƙofofin gidajenku, da a kan ƙofofinku,
21 That thy days may be multiplied, and the days of thy children in the land which the Lord swore to thy fathers, that he would give them as long as the heaven hangeth over the earth.
saboda kwanakinku da kwanakin’ya’yanku su yi tsawo a ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, muddin sama tana bisa duniya.
22 For if you keep the commandments which I command you, and do them, to love the Lord your God, and walk in all his ways, cleaving unto him,
In kuka lura, kuka kuma kiyaye dukan umarnai da nake ba ku, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya a hanyoyinsa, ku kuma riƙe shi gam,
23 The Lord will destroy all these nations before your face, and you shall possess them, which are greater and stronger than you.
Ubangiji zai kori dukan waɗannan al’ummai a gabanku, za ku kuma kore al’umman da suka fi ku yawa da ƙarfi.
24 Every place, that your foot shall tread upon, shall be yours. From the desert, and from Libanus, from the great river Euphrates unto the western sea shall be your borders.
Duk inda tafin ƙafanku ya taka, zai zama naku; iyakarku zai kama daga hamadan Lebanon da kuma daga Kogin Yuferites zuwa Bahar Rum.
25 None shall stand against you: the Lord your God shall lay the dread and fear of you upon all the land that you shall tread upon, as he hath spoken to you.
Babu mutumin da zai iya tsayayya da ku. Ubangiji Allahnku, zai sa razana da tsoronku a dukan ƙasar, a duk inda kuka tafi, kamar yadda ya alkawarta muku.
26 Behold I set forth in your sight this day a blessing and a curse:
Ga shi, a yau, ina sa a gabanku albarka da kuma la’ana,
27 A blessing, if you obey the commandments of the Lord your God, which I command you this day:
albarka in kun yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, da nake ba ku;
28 A curse, if you obey not the commandments of the Lord your. God, but revolt from the way which now I shew you, and walk after strange gods which you know not.
la’ana in ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku, kuka kuma juya daga hanyar da na umarce ku, ta wurin bin waɗansu alloli, waɗanda ba ku sani ba.
29 And when the Lord thy God shall have brought thee into the land, whither thou goest to dwell, thou shalt put the blessing upon mount Garizim, the curse upon mount Hebal:
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da za ku shiga ku ci gādonta, sai ku yi shelar albarkun nan a dutsen Gerizim, ku kuma yi na la’ana a dutsen Ebal.
30 Which are beyond the Jordan, behind the way that goeth to the setting of the sun, in the land of the Chanaanite who dwelleth in the plain country over against Galgala, which is near the valley that reacheth and entereth far.
Waɗannan duwatsu biyu suna a hayin Urdun, yamma da hanya a ƙasar Kan’aniyawa mazaunan Araba, kusa da Gilgal wajajen manyan itatuwan More.
31 For you shall pass over the Jordan, to possess the land, which the Lord your God will give you, that you may have it and possess it.
Kuna gab da ƙetare Urdun fa, ku shiga, ku kuma mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku. Sa’ad da kuka karɓe ta, kuka kuma zauna a can,
32 See therefore that you fulfill the ceremonies and judgments, which I shall set this day before you.
ku tabbata kun yi biyayya da dukan ƙa’idodi, da kuma dokokin da nake sawa a gabanku a yau.

< Deuteronomy 11 >