< Deuteronomy 1 >
1 These are the words, which Moses spoke to all Israel beyond the Jordan, in the plain wilderness, over against the Red Sea, between Pharan and Thophel and Laban and Haseroth, where there is very much gold:
Waɗannan su ne kalmomin da Musa ya yi wa dukan Isra’ila, a hamada gabas da Urdun, wato, Araba, ɗaura da Suf, tsakanin Faran da Tofel, Laban, Hazerot da Dizahab.
2 Eleven days’ journey from Horeb by the way of Mount Seir to Cadesbarne.
(Yakan ɗauki kwana goma sha ɗaya daga Horeb zuwa Kadesh Barneya ta hanyar Dutsen Seyir.)
3 In the fortieth year, the eleventh month, the first day of the month, Moses spoke to the children of Israel all that the Lord had commanded him to say to them:
A shekara ta arba’in, a rana ta fari ga wata na goma sha ɗaya, Musa ya yi shela ga Isra’ilawa game da dukan abin da Ubangiji ya umarta shi game da su.
4 After that he had slain Sehon king of the Amorrhites, who dwelt in Hesebon: and Og king of Basan who abode in Astaroth, and in Edrai,
Wannan ya faru bayan ya ci Sihon sarkin Amoriyawa wanda ya yi mulki a Heshbon da yaƙi. A Edireyi kuma ya ci Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot da yaƙi.
5 Beyond the Jordan in the land of Moab. And Moses began to expound the law, and to say:
Gabas da iyakar Mowab, Musa ya fara bayyana wannan doka, yana cewa,
6 The Lord our God spoke to us in Horeb, saying: You have stayed long enough in this mountain:
Ubangiji Allahnmu ya faɗa mana a Horeb cewa, “Daɗewarku a wannan dutse ya isa haka.
7 Turn you, and come to the mountain of the Amorrhites, and to the other places that are next to it, the plains and the hills and the vales towards the south, and by the sea shore, the land of the Chanaanites, and of Libanus, as far as the great river Euphrates.
Ku tashi, ku ci gaba zuwa ƙasar tudun Amoriyawa; ku tafi wurin dukan maƙwabta a cikin Araba, a cikin duwatsu, a gindin yammancin tuddai, a Negeb da kuma a ta kwaruruka, da ƙasar Kan’aniyawa da kuma zuwa Lebanon, har zuwa babban kogi, wato, Yuferites.
8 Behold, said he, I have delivered it to you: go in and possess it, concerning which the Lord swore to your fathers Abraham, Isaac, and Jacob, that he would give it to them, and to their seed after them.
Duba na riga na ba ku wannan ƙasa. Ku shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub, da kuma ga zuriyarsu bayansu.”
9 And I said to you at that time:
A wancan lokaci na faɗa muku cewa, “Ku kaya ne masu nauyi da ni kaɗai ba zan iya ɗauka ba.
10 I alone am not able to bear you: for the Lord your God hath multiplied you, and you are this day as the stars of heaven, for multitude.
Ubangiji Allahnku ya ƙara yawanku har yau kuka zama da yawa kamar taurari a sarari.
11 (The Lord God of your fathers add to this number many thousands, and bless you as he hath spoken.)
Bari Ubangiji, Allahn kakanninku yă ƙara yawanku sau dubu, yă kuma albarkace ku yadda ya yi alkawari!
12 I alone am not able to bear your business, and the charge of you and your differences.
Amma yaya zan ɗauka dukan damuwoyinku da nawayarku da kuma faɗace-faɗacenku duka ni kaɗai?
13 Let me have from among you wise and understanding men, and such whose conversation is approved among your tribes, that I may appoint them your rulers.
Ku zaɓi waɗansu masu hikima, masu ganewa, da kuma mutanen da ake girmama daga kowace kabilarku, zan kuma sa su a kanku.”
14 Then you answered me: The thing is good which thou meanest to do.
Kuka amsa mini, kuka ce, “Abin da ka ce za ka yi, yana da kyau.”
15 And I took out of your tribes men wise and honourable, and appointed them rulers, tribunes, and centurions, and officers over fifties, and over tens, who might teach you all things.
Saboda haka na ɗauko shugabannin kabilanku masu hikima, waɗanda suka saba da ma’amala da jama’a, na sa su shugabanni a gabanku, waɗansu suka zama shugabanni a kan dubu-dubu, waɗansu a kan ɗari-ɗari, waɗansu a kan hamsin-hamsin, waɗansu kuma a kan goma-goma. Na sa su zama shugabanni a kabilanku.
16 And I commanded them, saying: Hear them, and judge that which is just: whether he be one of your country, or a stranger.
Na kuma umarci alƙalanku a wancan lokaci, na ce, “Ku yi adalci cikin shari’a tsakanin’yan’uwanku, ko damuwar tana tsakanin’yan’uwa Isra’ilawa ne, ko kuwa tsakanin Isra’ilawa da baƙin da suke zaune a cikinku.
17 There shall be no difference of persons, you shall hear the little as well as the great: neither shall you respect any man’s person, because it is the judgment of God. And if any thing seem hard to you, refer it to me, and I will hear it.
Kada ku nuna sonkai a cikin hukuncinku, ku saurari kowane ɓangare, babba da ƙarami, kada ku ji tsoron wani, gama hukunci na Allah ne. Ku kawo kowane batun da ya sha ƙarfinku, zan kuwa saurare shi.”
18 And I commanded you all things that you were to do.
A wancan lokacin kuwa na faɗa muku dukan abin da ya kamata ku yi.
19 And departing from Horeb, we passed through the terrible and vast wilderness, which you saw, by the way of the mountain of the Amorrhite, as the Lord our God had commanded us. And when we were come into Cadesbarne,
Sa’an nan, muka kama hanya daga Horeb muka ratsa wajen ƙasar tudun Amoriyawa ta dukan hamadarta mai fāɗi, da kuma mai bantsoron da kuka gani, muka kuma kai Kadesh Barneya yadda Ubangiji, Allahnmu ya umarce mu.
20 I said to you: You are come to the mountain of the Amorrhite, which the Lord our God will give to us.
Sai na ce muku, “Kun iso ƙasar tudun Amoriyawa, wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.
21 See the land which the Lord thy God giveth thee: go up and possess it, as the Lord our God hath spoken to thy fathers: fear not, nor be any way discouraged.
Duba, Ubangiji Allahnku ya ba ku ƙasar. Ku haura ku mallake ta yadda Ubangiji Allahn kakanninku ya faɗa muku. Kada ku ji tsoro, kada ku fid da zuciya.”
22 And you came all to me, and said: Let us send men who may view the land, and bring us word what way we shall go up, and to what cities we shall go.
Sai dukanku kuka zo wurina kuka ce, “Bari mu aiki mutane su yi gaba su leƙi mana asirin ƙasar, su kuma kawo mana labari game da hanyar da za mu bi, da kuma biranen da za mu shiga.”
23 And because the saying pleased me, I sent of you twelve men, one of every tribe:
Ra’ayin nan naku ya yi mini kyau, saboda haka na zaɓe ku goma sha biyu, mutum guda daga kowace kabila.
24 Who, when they had set forward and had gone up to the mountains, came as far as the valley of the cluster: and having viewed the land,
Suka tafi, suka haura zuwa ƙasar tudu, suka kai Kwarin Eshkol, suka leƙo asirin ƙasar.
25 Taking of the fruits thereof, to shew its fertility, they brought them to us, and said: The land is good, which the Lord our God will give us.
Suka ɗebi’ya’yan itatuwan ƙasar, suka sauko mana da su, suka kuma ba da labari cewa, “Ƙasar da Ubangiji Allahnmu yake ba mu, kyakkyawa ce.”
26 And you would not go up, but being incredulous to the word of the Lord our God,
Amma ba ku yi niyya ku haura ba, kuka yi tawaye gāba da umarnin Ubangiji Allahnku.
27 You murmured in your tents, and said: The Lord hateth us, and therefore he hath brought us out of the land of Egypt, that he might deliver us into the hand of the Amorrhite, and destroy us.
Kuka yi gunaguni a cikin tentunanku, kuna cewa, “Ubangiji ya ƙi mu; shi ya sa ya fitar da mu daga Masar don yă ba da mu ga hannuwan Amoriyawa su hallaka mu.
28 Whither shall we go up? the messengers have terrified our hearts, saying: The multitude is very great, and taller than we: the cities are great, and walled up to the sky, we have seen the sons of the Enacims there.
Ina za mu?’Yan’uwanmu suka sa muka fid da zuciya. Suka ce, ‘Mutanen sun fi mu ƙarfi, sun kuma fi mu tsayi; biranen manya ne, da katanga har sama. Mun ma ga Anakawa a can.’”
29 And I said to you: Fear not, neither be ye afraid of them:
Sai na ce muku, “Kada ku firgita; kada ku ji tsoronsu.
30 The Lord God, who is your leader, himself will fight for you, as he did in Egypt in the sight of all.
Ubangiji Allahnku yana a gabanku, zai yi yaƙi saboda ku, kamar yadda ya yi a kan idanunku a Masar,
31 And in the wilderness (as thou hast seen) the Lord thy God hath carried thee, as a man is wont to carry his little son, all the way that you have come, until you came to this place.
da kuma a cikin hamada. A can ma kun ga yadda Ubangiji Allahnku ya riƙe ku ko’ina da kuka tafi, kamar yadda mahaifi yakan riƙe ɗansa, sai da kuka kai wannan wuri.”
32 And yet for all this you did not believe the Lord your God,
Duk da haka, ba ku amince da Ubangiji Allahnku ba,
33 Who went before you in the way, and marked out the place, wherein you should pitch your tents, in the night shewing you the way by fire, and in the day by the pillar of a cloud.
shi da ya sha gabanku a tafiyarku, cikin wuta da dad dare da kuma girgije da rana, don yă nemi wurare domin ku kafa sansani, don kuma yă nuna muku hanyar da za ku bi.
34 And when the Lord had heard the voice of your words, he was angry and swore, and said:
Da Ubangiji ya ji abin da kuka faɗa, sai ya husata, ya kuma yi rantsuwa ya ce,
35 Not one of the men of this wicked generation shall see the good land, which I promised with an oath to your fathers:
“Babu wani a cikin wannan muguwar tsara da zai ga ƙasa mai kyau da na rantse zan ba wa kakanninku,
36 Except Caleb the son of Jephone: for he shall see it, and to him I will give the land that he hath trodden upon, and to his children, because he hath followed the Lord.
sai dai Kaleb ɗan Yefunne. Zai gan ta, zan ba shi duk ƙasar da tafin ƙafarsa ta taka, shi da zuriyarsa, gama ya bi Ubangiji da zuciya ɗaya.”
37 Neither is his indignation against the people to be wondered at, since the Lord was angry with me also on your account, and said: Neither shalt thou go in thither.
Saboda ku Ubangiji ya husata da ni, ya kuma ce, “Kai ma, ba za ka shiga ƙasar ba.
38 But Josue the son of Nun, thy minister, he shall go in for thee: exhort and encourage him, and he shall divide the land by lot to Israel.
Amma mataimakinka, Yoshuwa ɗan Nun, zai shiga. Ka ƙarfafa shi gama shi ne zai jagoranci Isra’ila su gāje ta.
39 Your children, of whom you said that they should be led away captives, and your sons who know not this day the difference of good and evil, they shall go in: and to them I will give the land, and they shall possess it.
Amma’ya’yanku ƙanana waɗanda ba su san mugunta ko nagarta ba, waɗanda kuke tsammani za a kwashe su ganima, su za su shiga ƙasar. Zan ba da ita gare su, za su kuwa mallake ta.
40 But return you and go into the wilderness by the way of the Red Sea.
Amma ku kam, sai ku juya, ku koma cikin hamada ta hanyar Jan Teku.”
41 And you answered me: We have sinned against the Lord: we will go up and fight, as the Lord our God hath commanded. And when you went ready armed unto the mountain,
Sai kuka amsa, kuka ce, “Mun yi zunubi ga Ubangiji. Za mu haura mu yi yaƙi yadda Ubangiji Allahnmu ya umarce mu.” Saboda haka kowannenku ya yi ɗamara da kayan yaƙinsa, kuka yi tsammani zai zama muku da sauƙi ku ci ƙasar tuddai da yaƙi.
42 The Lord said to me: Say to them: Go not up, and fight not, for I am not with you: lest you fall before your enemies.
Amma Ubangiji ya ce mini, “In faɗa muku, ‘Kada ku fāɗa musu da yaƙi, gama ba zai kasance tare da ku ba. Idan kuka kuskura, abokan gābanku za su murƙushe ku.’”
43 I spoke, and you hearkened not: but resisting the commandment of the Lord, and swelling with pride, you went up into the mountain.
Sai na faɗa muku, amma ba ku saurara ba. Kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji, a cikin jahilcinku kuwa kuka taka, kuka haura cikin ƙasar tudu.
44 And the Amorrhite that dwelt in the mountains coming out, and meeting you, chased you, as bees do: and made slaughter of you from Seir as far as Horma.
Amoriyawan da suke zama a waɗannan tuddai, suka fito kamar tarin ƙudan zuma gāba da ku, suka kore ku, suka fatattake ku daga Seyir har zuwa Horma.
45 And when you returned and wept before the Lord, he heard you not, neither would he yield to; your voice.
Kuka dawo, kuka yi kuka a gaban Ubangiji, amma bai kula da ku ba, balle yă saurare ku.
46 So you abode in Cadesbarne a long time.
Haka kuwa kuka zauna a Kadesh kwanaki masu yawa, kuka ci lokaci a can.