< Amos 4 >
1 Hear this word, ye fat kine that are in the mountains of Samaria: you that oppress the needy, and crush the poor: that say to your masters: Bring, and we will drink.
Ku kasa kunne ga wannan, ya ku shanun Bashan a kan Dutsen Samariya, ku matan da kuke cin zalin matalauta, kuke kuma danne matalauta, kuna kuma ce wa mazanku, “Ku kawo mana abin sha!”
2 The Lord God hath sworn by his holiness, that lo, the days shall come upon you, when they shall lift you up on pikes, and what shall remain of you in boiling pots.
Ubangiji Mai Iko Duka ya rantse da tsarkinsa. “Tabbatacce lokaci yana zuwa da za a jawo ku da ƙugiyoyi, na ƙarshenku za a kama da ƙugiyar kifi.
3 And you shall go out at the breaches one over against the other, and you shall be cast forth into Armon, saith the Lord.
Dukanku za ku wuce ta kai tsaye ta inda katangar ta tsage, za a jefar da ku a Harmon,” in ji Ubangiji.
4 Come ye to Bethel, and do wickedly: to Galgal, and multiply transgressions: and bring in the morning your victims, your tithes in three days.
“Ku tafi Betel ku yi ta aikata zunubi; ku je Gilgal ku ƙara yin zunubi. Ku kawo hadayunku kowace safiya, zakkarku kowace shekara uku.
5 And offer a sacrifice of praise with leaven: and call free offerings, and proclaim it: for so you would do, O children of Israel, saith the Lord God.
Ku ƙona burodinku mai yisti kamar hadaya ta godiya, ku yi fariya game da hadayunku na yarda rai, ku yi taƙama game da su, ya ku Isra’ilawa, gama abin da kuke jin daɗin aikata ke nan,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
6 Whereupon I also have given you dulness of teeth in all your cities, and want of bread in all your places: yet you have not returned to me, saith the Lord.
“Na bar ku da yunwa a kowace birni, da kuma rashin abinci a kowane gari, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
7 I also have withholden the rain from you, when there were yet three months to the harvest: and I caused it to rain upon one city, and caused it not to rain upon another city: one piece was rained upon: and the piece whereupon I rained not, withered.
“Na kuma hana muku ruwan sama tun shuke-shuken suna wata uku kafin lokacin girbi. Na sa aka yi ruwan sama a wani gari, sai na hana a yi a wani gari. Wata gona ta sami ruwan sama; wata gona kuma ta bushe.
8 And two and three cities went to one city to drink water, and were not filled: yet you returned not to me, saith the Lord.
Mutane suna tangaɗi daga gari zuwa gari suna neman ruwa amma ba su sami isashen ruwan sha ba, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
9 I struck you with a burning wind, and with mildew, the palmerworm hath eaten up your many gardens, and your vineyards: your olive groves, and fig groves: yet you returned not to me, saith the Lord.
“Sau da yawa na ɓata gonakinku da fumfuna da kuma cuta. Fāri suka cinye itatuwanku na inabi da na ɓaure, da na zaitun duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
10 I sent death upon you in the way of Egypt, I slew your young men with the sword, even to the captivity of your horses: and I made the stench of your camp to come up into your nostrils: yet you returned not to me, saith the Lord.
“Na aiko muku annoba yadda na yi a Masar. Na karkashe samarinku da takobi, tare da kamammun dawakanku. Na cika hancinku da warin sansaninku, duk da haka ba ku juyo gare ni ba” in ji Ubangiji.
11 I destroyed some of you, as God destroyed Sodom and Gomorrha, and you were as a firebrand plucked out of the burning: yet you returned not to me, saith the Lord.
“Na hallaka waɗansunku kamar yadda na hallaka Sodom da Gomorra. Kuna kama da itace mai cin wutar da na cire daga cikin wuta, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,” in ji Ubangiji.
12 Therefore I will do these things to thee, O Israel: and after I shall have done these things to thee, be prepared to meet thy God, O Israel.
“Saboda haka ga abin da zan yi da ku, ya Isra’ila, don kuwa zan yi muku haka, sai ku yi shirin gamuwa da Allahnku, ya Isra’ila.”
13 For behold he that formeth the mountains and createth the wind, and declareth his word to man, he that maketh the morning mist, and walketh upon the high places of the earth: the Lord the God of hosts is his name.
Shi wanda ya yi duwatsu, ya halicci iska, ya kuma bayyana wa mutum tunaninsa, shi wanda ya juya safiya ta zama duhu yana takawa a wurare masu tsawo na duniya, Ubangiji Allah Maɗaukaki ne sunansa.