< 2 Samuel 22 >
1 And David spoke to the Lord the words of this canticle, in the day that the Lord delivered him out of the hand of all his enemies, and out of the hand of Saul,
Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
2 And he said: The Lord is my rock, and my strength, and my saviour.
Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
3 God is my strong one, in him will I trust: my shield, and the horn of my salvation: he lifteth me up, and is my refuge: my saviour, thou wilt deliver me from iniquity.
Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
4 I will call on the Lord who is worthy to be praised: and I shall be saved from my enemies.
“Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
5 For the pangs of death have surrounded me: the floods of Belial have made me afraid.
Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
6 The cords of hell compassed me: the snares of death prevented me. (Sheol )
Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol )
7 In my distress I will call upon the Lord, and I will cry to my God: and he will hear my voice out of his temple, and my cry shall come to his ears.
“A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
8 The earth shook and trembled, the foundations of the mountains were moved, and shaken, because he was angry with them.
Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
9 A smoke went up from his nostrils, and a devouring fire out of his mouth: coals were kindled by it.
Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
10 He bowed the heavens, and came down: and darkness was under his feet.
Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
11 And he rode upon the cherubims, and flew: and slid upon the wings of the wind.
Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
12 He made darkness a covering round about him: dropping waters out of the clouds of the heavens.
Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
13 By the brightness before him, the coals of fire were kindled.
Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
14 The Lord shall thunder from heaven: and the most high shall give forth his voice.
Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
15 He shot arrows and scattered them: lightning, and consumed them.
Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
16 And the overflowings of the sea appeared, and the foundations of the world were laid open at the rebuke of the Lord, at the blast of the spirit of his wrath.
Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
17 He sent from on high, and took me, and drew me out of many waters.
“Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
18 He delivered me from my most mighty enemy, and from them that hated me: for they were too strong for me.
Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
19 He prevented me in the day of my affliction, and the Lord became my stay.
Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
20 And he brought me forth into a large place, he delivered me, because I pleased him.
Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
21 The Lord will reward me according to my justice: and according to the cleanness of my hands he will render to me.
“Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
22 Because I have kept the ways of the Lord, and have not wickedly departed from my God.
Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
23 For all his judgments are in my sight: and his precepts I have not removed from me.
Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
24 And I shall be perfect with him: and shall keep myself from my iniquity.
Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
25 And the Lord will recompense me according to my justice: and according to the cleanness of my hands in the sight of his eyes.
Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
26 With the holy one thou wilt be holy: and with the valiant perfect.
“Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
27 With the elect thou wilt be elect: and with the perverse thou wilt be perverted.
ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
28 And the poor people thou wilt save: and with thy eyes thou wilt humble the haughty.
Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
29 For thou art my lamp, O Lord: and thou, O Lord, wilt enlighten my darkness.
Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
30 For in thee I will run girded: in my God I will leap over the wall.
Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
31 God, his way is immaculate, the word of the Lord is tried by fire: he is the shield of all that trust in him.
“Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
32 Who is God but the Lord: and who is strong but our God?
Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
33 God who hath girded me with strength, and made my way perfect.
Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
34 Making my feet like the feet of harts, and setting me upon my high places.
Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
35 He teacheth my bands to war: and maketh my arms like a bow of brass.
Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
36 Thou hast given me the shield of my salvation: and thy mildness hath multiplied me.
Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
37 Thou shalt enlarge my steps under me: and my ankles shall not fail.
Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
38 I will pursue after my enemies, and crush them: and will not return again till I consume them.
“Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
39 I will consume them and break them in pieces, so that they shall not rise: they shall fall under my feet.
Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
40 Thou hast girded me with strength to battle: thou hast made them that resisted me to bow under me.
Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
41 My enemies thou hast made to turn their back to me: them that hated me, and I shall destroy them.
Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
42 They shall cry, and there shall be none to save: to the Lord, and he shall not hear them.
Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
43 I shall beat them as small as the dust of the earth: I shall crush them and spread them abroad like the mire of the streets.
Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
44 Thou wilt save me from the contradictions of my people: thou wilt keep me to be the head of the Gentiles: the people which I know not, shall serve me,
“Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
45 The sons of the stranger will resist me, at the hearing of the ear they will obey me.
baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
46 The strangers are melted away, and shall be straitened in their distresses.
Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
47 The Lord liveth, and my God is blessed: and the strong God of my salvation shall be exalted:
“Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
48 God who giveth me revenge, and bringest down people under me,
Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
49 Who bringest me forth from my enemies, and liftest me up from them that resist me: from the wicked man thou shalt deliver me.
wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
50 Therefore will I give thanks to thee. O Lord, among the Gentiles, and will sing to thy name.
Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
51 Giving great salvation to his king, and shewing mercy to David his anointed, and to his seed for ever.
“Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”