< 2 Kings 6 >
1 And the sons of the prophets said to Eliseus: Behold the place where we dwell with thee is too strait for us.
Sai ƙungiyar annabawa suka ce wa Elisha, “Duba, wurin da muke taruwa ya kāsa mana.
2 Let us go as far as the Jordan and take out of the wood every man a piece of timber, that we may build us there a place to dwell in. And he said: Go.
Bari mu je Urdun, inda kowannenmu zai saro itace; mu gina inda za mu zauna.” Sai ya ce musu, “Ku je.”
3 And one of them said: But come thou also with thy servants. He answered: I will come.
Sai ɗayansu ya ce, “Ba za ka zo tare da bayinka ba?” Sai Elisha ya ce “Zan zo.”
4 So he went with them. And when they were come to the Jordan they cut down wood.
Ya kuma tafi tare da su. Suka tafi Urdun suka fara saran itatuwa.
5 And it happened, as one was felling some timber, that the head of the axe fell into the water: and he cried out, and said: Alas, alas, alas, my lord, for this same was borrowed.
Yayinda ɗayansu yake cikin saran itace, sai kan gatarin ya fāɗi a ruwa, sai ya ce, “Kash, ranka yă daɗe, kayan aro ne fa!”
6 And the man of God said: Where did it fall? and he shewed him the place. Then he cut off a piece of wood, and cast it in thither: and the iron swam.
Sai mutumin Allah ya ce, “Daidai ina ya fāɗa?” Da ya nuna masa wurin, sai Elisha ya yanka ɗan sanda ya jefa a wurin, ya sa kan gatarin ya taso sama.
7 And he said: Take it up. And he put out his hand and took it.
Sai ya ce masa, “Ka ɗauko.” Sai mutumin ya miƙa hannu ya ɗauka.
8 And the king of Syria warred against Israel, and took counsel with his servants, saying: In such and such a place let us lay ambushes.
To, fa, sarkin Aram yana yaƙi da Isra’ila. Bayan ya tattauna da hafsoshinsa, sai ya ce, “Zan kafa sansanina a wurin kaza da kaza.”
9 And the man of God sent to the king of Israel, saying: Beware that thou pass not to such a place: for the Syrians are there in ambush.
Sai mutumin Allah ya aika wa sarkin Isra’ila cewa, “Ka yi hankali da wuce wuri kaza, domin Arameyawa za su gangara can.”
10 And the king of Israel sent to the place which the man of God had told him, and prevented him, and looked well to himself there not once nor twice.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya lura da inda mutumin Allah ya ambata. Sau da sau Elisha yakan yi wa sarki kashedi, don haka ya riƙa taka yi tsantsan a wuraren nan.
11 And the heart of the king of Syria was troubled for this thing. And calling together his servants, he said: Why do you not tell me who it is that betrays me to the king of Israel?
Wannan ya husata sarkin Aram. Ya kira hafsoshinsa ya tambaye su ya ce, “Ku faɗa mini, wane ne a cikinmu yake gefen sarkin Isra’ila?”
12 And one of his servants said: No one, my lord O king: but Eliseus the prophet, that is in Israel, telleth the king of Israel all the words, that thou speakest in thy privy chamber.
Sai ɗaya daga cikin hafsoshinsa ya ce, “Babu waninmu, ranka yă daɗe; Elisha, annabin da yake a Isra’ila ne, yake faɗa wa sarkin Isra’ila dukan zancen da ka yi a ɗakinka.”
13 And he said to them: Go, and see where he is: that I may send, and take him. And they told him, saying: Behold he is in Dothan.
Sai sarki ya ba da umarni ya ce, “Ku je ku tabbatar da inda yake don in aika mutane a kamo shi.” Sai ya sami rahoto cewa, “Yana a Dotan.”
14 Therefore he sent thither horses and chariots, and the strength of an army: and they came by night, and beset the city.
Sai ya aika da dawakai da kekunan yaƙi da babban rukunin soja zuwa can. Suka bi dare, suka kewaye birnin.
15 And the servant of the man of God rising early, went out, and saw an army round about the city, and horses and chariots: and he told him, saying: Alas, alas, alas, my lord, what shall we do?
Sa’ad da bawan mutumin Allah ya farka ya kuma fita kashegari da sassafe, sai ga mayaƙa tare da dawakai da kekunan yaƙi sun kewaye birni. Sai bawan ya ce, “Ranka yă daɗe! Me za mu yi?”
16 But he answered: Fear not: for there are more with us than with them.
Sai annabin ya ce, “Kada ka ji tsoro, waɗanda suke tare da mu sun fi waɗanda suke tare da su.”
17 And Eliseus prayed, and said: Lord, open his eyes, that he may see. And the Lord opened the eyes of the servant, and he saw: and behold the mountain was full of horses, and chariots of fire round about Eliseus.
Sa’an nan Elisha ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji, ka buɗe idanunsa yă gani!” Sai Ubangiji ya buɗe idanun bawan, ya duba, ya ga tuddai cike da dawakai da keken yaƙin wuta kewaye da Elisha.
18 And the enemies came down to him, but Eliseus prayed to the Lord, saying: Strike, I beseech thee, this people with blindness. And the Lord struck them with blindness, according to the word of Eliseus.
Yayinda abokan gāba suka gangaro wajensa, sai Elisha ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ka sa mutanen nan su zama makafi.” Sai Ubangiji ya buge su da makanta kamar yadda Elisha ya roƙa.
19 And Eliseus said to them: This is not the way, neither is this the city: follow me, and I will shew you the man whom you seek. So he led them into Samaria.
Elisha ya ce musu, “Wannan ba ita ce hanyar ba, ba kuma gari ke nan ba, ku bi ni, zan kuwa kai ku wurin mutumin da kuke nema!” Sai ya kai su Samariya.
20 And when they were come into Samaria, Eliseus said: Lord, open the eyes of these men, that they may see. And the Lord opened their eyes, and they saw themselves to be in the midst of Samaria.
Bayan suka shiga birnin, sai Elisha ya ce, “Ubangiji, ka buɗe idanun mutanen nan don su gani.” Sa’an nan Ubangiji ya buɗe idanunsu suka ga kansu a tsakiyar Samariya.
21 And the king of Israel said to Eliseus, when he saw them: My father, shall I kill them?
Da sarkin Isra’ila ya gan su, sai ya tambayi Elisha ya ce, “In kashe su ne, mahaifina? In kashe su?”
22 And he said: Thou shalt not kill them: for thou didst not take them with thy sword, or thy bow, that thou mayst kill them: but set bread and water before them, that they may eat and drink, and go to their master.
Elisha ya ce, “Kada ka kashe su. Za ka kashe mutanen da ka kame da takobi ko bakanka? Ka ba su abinci da ruwa su ci, su sha, sa’an nan su koma wurin maigidansu.”
23 And a great provision of meats was set before them, and they ate and drank, and he let them go, and they went away to their master, and the robbers of Syria came no more into the land of Israel.
Saboda haka aka shirya musu babban liyafa, bayan sun ci, suka kuma sha, sai ya tura su zuwa wurin maigidansu. Ta haka’yan harin Aram suka daina kai hari a yankin Isra’ila.
24 And it came to pass after these things, that Benadad king of Syria gathered together all his army, and went up, and besieged Samaria.
Bayan wani lokaci, Ben-Hadad sarkin Aram ya tattara dukan rundunarsa, ya je ya kewaye Samariya da yaƙi.
25 And there was a great famine in Samaria: and so long did the siege continue, till the head of an ass was sold for fourscore pieces of silver, and the fourth part of a cabe of pigeon’s dung, for five pieces of silver.
Aka yi babban yunwa a cikin birnin. Saboda daɗewar wannan kewayewar da aka yi wa birnin, sai yunwa ta ɓarke a birnin, har ana sayar da kan jaki a kan shekel tamanin, kashin kurciya kuma a kan shekel biyar.
26 And as the king of Israel was passing by the wall, a certain woman cried out to him, saying: Save me, my lord O king.
Yayinda sarkin Isra’ila yake wucewa kusa da katanga, sai wata mace ta yi masa kuka ta ce, “Ka taimake ni, ranka yă daɗe, sarki!”
27 And he said: If the Lord doth not save thee, how can I save thee? out of the barnfloor, or out of the winepress? And the king said to her: What aileth thee? And she answered:
Sai sarki ya amsa ya ce, “In Ubangiji bai taimake ki ba, me zan iya yi? Ina da hatsi ko ruwan inabin da zan ba ki ne?”
28 This woman said to me: Give thy son, that we may eat him today, and we will eat my son tomorrow.
Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Me ya faru?” Sai ta amsa ta ce, “Wannan mace ta ce mini, ‘Kawo ɗanki mu ci yau, gobe kuwa mu ci ɗana.’
29 So we boiled my son, and ate him. And I said to her on the next day: Give thy son that we may eat him. And she hath hid her son.
Saboda haka muka dafa ɗana muka ci. Kashegari na ce mata, ‘Kawo ɗanki mu ci,’ amma ta ɓoye shi.”
30 When the king heard this, he rent his garments, and passed by upon the wall. And all the people saw the haircloth which he wore within next to his flesh.
Da sarki ya ji maganar macen sai ya yage rigunansa. Sa’ad da sarki yake wucewa a kan katangar birnin, sai mutane suka gan yana saye da rigar makoki a ciki.
31 And the king said: May God do so and so to me, and may he add more, if the head of Eliseus the son of Saphat shall stand on him this day.
Ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani har ma fiye da haka, idan ban cire kan Elisha ɗan Shafat yau ba!”
32 But Eliseus sat in his house, and the ancients sat with him. So he sent a man before: and before that messenger came, he said to the ancients: Do you know that this son of a murderer hath sent to cut off my head? Look then, when the messenger shall come, shut the door, and suffer him not to come in: for behold the sound of his master’s feet is behind him.
To, Elisha yana zaune a cikin gidansa, dattawa kuwa suna zaune tare da shi. Sai sarki ya aiki ɗan aika yă ci gaba, amma kafin ɗan aikan yă isa, Elisha ya ce wa dattawan, “Kun gani ko? Wannan mai kisa ya aiko a cire mini kai! To, idan ɗan aikan ya iso, sai ku rufe ƙofar da ƙarfi, ku bar shi a waje. Ba da jimawa ba, maigidansa zai bi bayansa?”
33 While he was yet speaking to them, the messenger appeared who was coming to him. And he said: Behold, so great an evil is from the Lord: what shall I look for more from the Lord?
Yana magana da su ke nan, sai ga ɗan aikan ya gangaro wajensa. Sarki kuma ya ce, “Wannan bala’in daga wurin Ubangiji ya fito. Don me zan sa zuciya ga Ubangiji kuma?”