< 2 Kings 14 >
1 In the second year of Joas son of Joachaz, king of Israel, reigned Amasias son of Joas king of Juda.
A shekara ta biyu ta mulkin Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila, Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya fara mulki.
2 He was five and twenty years old when he began to reign: and nine and twenty years he reigned in Jerusalem: the name of his mother was Joadan of Jerusalem.
Ya zama sarki yana da shekaru ashirin da biyar, ya kuma yi mulki a Urushalima shekaru ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin, mutuniyar Urushalima.
3 And he did that which was right before the Lord, but yet not like David his father. He did according to all things that Joas his father did:
Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, sai dai ba kamar kakansa Dawuda ba. A kome dai ya bi gurbin mahaifinsa Yowash.
4 But this only, that he took not away the high places: for yet the people sacrificed and burnt incense in the high places.
Ba a dai kawar da masujadan kan tudu ba; mutane suka ci gaba da yin hadaya da ƙone turare a can.
5 And when he had possession of the kingdom, he put his servants to death that had slain the king his father:
Bayan masarauta ta kahu a hannunsa, sai ya kashe fadawan da suka kashe mahaifinsa sarki.
6 But the children of the murderers he did not put to death, according to that which is written in the book of the law of Moses, wherein the Lord commanded, saying: The fathers shall not be put to death for the children, neither shall the children be put to death for the fathers: but every man shall die for his own sins.
Duk da haka bai kashe’ya’yan masu kisan ba, bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda laifin’ya’ya ba, ko kuma’ya’ya saboda laifin iyayensu ba, kowa zai mutu don zunubansa.”
7 He slew of Edom in the valley of the Saltpits ten thousand men, and took the rock by war, and called the name thereof Jectehel, unto this day.
Shi ne kuma wanda ya ci mutanen Edom dubu goma a yaƙi, a Kwarin Gishiri, ya kuma ci Sela da yaƙi, ya ba ta suna Yokteyel, sunan da ake kiranta har wa yau.
8 Then Amasias sent messengers to Joas son of Joachaz, son of Jehu king of Israel, saying: Come let us see one another.
Sai Amaziya ya aika’yan aika wurin Yehowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, yana tsokanarsa cewa, “Zo, mu sadu fuska da fuska.”
9 And Joas king of Israel sent again to Amasias king of Juda, saying: A thistle of Libanus sent to a cedar tree, which is in Libanus, saying: Give thy daughter to my son to wife. And the beasts of the forest, that are in Libanus, passed and trod down the thistle.
Amma Yehowash sarkin Isra’ila ya mai da martani wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata’yar ƙaya a kurmin Lebanon ta aika da saƙo wurin itacen al’ul a Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Amma wani naman jeji ya zo ya tattake ƙayar.
10 Thou hast beaten and prevailed over Edom, and thy heart hath lifted thee up: be content with the glory, and sit at home: why provokest thou evil, that thou shouldst fall, and Juda with thee?
Tabbatacce ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana ɗaga kai. To, ka gode da darajar da ka samu, amma ka zauna a gida! Don me kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da kuma ta Yahuda?”
11 But Amasias did not rest satisfied. So Joas king of Israel went up, and he and Amasias king of Juda saw one another in Bethsames a town in Juda.
Amma Amaziya bai saurara ba, saboda haka Yehowash sarkin Isra’ila ya kai masa hari. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh.
12 And Juda was put to the worst before Israel, and they fled every man to their dwellings.
Isra’ila suka fatattaki Yahuda, kowa kuwa ya tsere zuwa gidansa.
13 But Joas king of Israel took Amasias, king of Juda the son of Joas, the son of Ochozias, in Bethsames, and brought him into Jerusalem: and he broke down the wall of Jerusalem, from the gate of Ephraim to the gate of the corner, four hundred cubits.
Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya, a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya tafi Urushalima ya rushe katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, ratarta ta kai wajen ƙafa ɗari shida.
14 And he took all the gold, and silver, and all the vessels, that were found in the house of the Lord, and in the king’s treasures, and hostages, and returned to Samaria.
Ya kwashi ɗaukan zinariya da azurfa da duk kayan da aka samu a haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin fadan. Ya kuma kwashi bayi sa’an nan ya koma Samariya.
15 But the rest of the acts of Joas, which he did, and his valour, wherewith he fought against Amasias king of Juda, are they not written in the book of the words of the days of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehowash, abin da ya yi da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙinsa da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
16 And Joas slept with his fathers, and was buried in Samaria, with the kings of Israel: and Jeroboam his son reigned in his stead.
Ya huta da kakanninsa aka kuma binne shi a Samariya tare da sarakunan Isra’ila. Yerobowam ɗansa, ya kuma gāje shi.
17 And Amasias the son of Joas king of Juda lived, after the death of Joas son of Joachaz king of Israel fifteen years.
Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya yi shekaru goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
18 And the rest of the acts of Amasias, are they not written in the book of the words of the days of the kings of Juda?
Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
19 Now they made a conspiracy against him in Jerusalem: and he fled to Lachis. And they sent after him to Lachis, and killed him there.
Suka ƙulla masa maƙarƙashiya a Urushalima, ya gudu zuwa Lakish, amma suka aika har Lakish aka kashe shi a can.
20 And they brought him away upon horses, and he was buried in Jerusalem with his fathers in the city of David.
Aka ɗauko shi a kan doki aka kawo shi Urushalima, aka kuwa binne shi tare da kakanninsa, a Birnin Dawuda.
21 And all the people of Juda took Azarias, who was sixteen years old, and made him king instead of his father Amasias.
Sa’an nan dukan mutanen Yahuda suka ɗauki Azariya, wanda yake ɗan shekaru goma sha shida da haihuwa, suka naɗa shi sarki a madadin mahaifinsa Amaziya.
22 He built Elath, and restored it to Juda, after that the king slept with his fathers.
Shi ne ya sāke gina Elat, ya kuma maido da ita a hannun Yahuda bayan Amaziya ya huta da kakanninsa.
23 In the fifteenth year of Amasias son of Joas king of Juda, reigned Jeroboam the son of Joas king of Israel in Samaria, one and forty years:
A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yehowash sarkin Isra’ila ya zama sarki a Samariya, ya kuma yi mulki na shekaru arba’in da ɗaya.
24 And he did that which was evil before the Lord. He departed not from all the sins of Jeroboam the son of Nabat, who made Israel to sin.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji bai kuwa kauce wa duk zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
25 He restored the borders of Israel from the entrance of Emath, unto the sea of the wilderness, according to the word of the Lord the God of Israel, which he spoke by his servant Jonas the son of Amathi, the prophet, who was of Geth, which is in Opher.
Shi ne ya maido da iyakokin Isra’ila daga Lebo Hamat zuwa Tekun Araba, bisa ga maganar Ubangiji, Allah na Isra’ila, da ya yi ta bakin bawansa Yunana ɗan Amittai, annabi daga Gat-Hefer.
26 For the Lord saw the affliction of Israel that it was exceeding bitter, and that they were consumed even to them that were shut up in prison, and the lowest persons, and that there was no one to help Israel.
Ubangiji ya ga irin muguwar wahalar da ta shafi kowa a Isra’ila, ko bawa ko’yantacce, babu mai taimakonsu.
27 And the Lord did not say that he would blot out the name of Israel from under heaven, but he saved them by the hand of Jeroboam the son of Joas.
Da yake kuma Ubangiji bai ce zai shafe sunan Isra’ila daga fuskar duniya ba, sai ya cece su ta hannun Yerobowam ɗan Yowash.
28 But the rest of the acts of Jeroboam, and all that he did, and his velour, wherewith he fought, and how he restored Damascus, and Emath to Juda in Israel, are they not written in the book of the words of the days of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yerobowam, da dukan abin da ya yi, da yaƙe-yaƙen da ya yi, haɗe da sāke ƙwato wa Isra’ila Damaskus da Hamat waɗanda suke a hannun Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
29 And Jeroboam slept with his fathers the kings of Israel, and Zacharias his son reigned in his stead.
Yerobowam ya huta da kakanninsa, sarakunan Isra’ila. Zakariya ɗansa kuwa ya gāje shi.