< 2 Kings 13 >

1 In the three and twentieth year of Joas son of Ochozias king of Juda, Joachaz the son of Jehu reigned over Israel in Samaria, seventeen years.
A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
2 And he did evil before the Lord, and followed the sins of Jeroboam the son of Nabat, who made Israel to sin, and he departed not from them.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
3 And the wrath of the Lord was kindled against Israel, and he delivered them into the hand of Hazael the king of Syria, and into the hand of Benadad the son of Hazael all days.
Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
4 But Joachaz besought the face of the Lord, and the Lord heard him: for he saw the distress of Israel, because the king of Syria had oppressed them:
Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
5 And the Lord gave Israel a saviour, and they were delivered out of the hand of the king of Syria: and the children of Israel dwelt in their pavilions as yesterday and the day before.
Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
6 But yet they departed not from the sins of Jeroboam, who made Israel to sin, but walked in them: and there still remained a grove also in Samaria.
Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
7 And Joachaz had no more left of the people than fifty horsemen, and ten chariots, and ten thousand footmen: for the king of Syria had slain them, and had brought them low as dust by thrashing in the barnfloor.
Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
8 Rut the rest of the acts of Joachaz, and all that he did, and his valour, are they not written in the book of the words of the days of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
9 And Joachaz slept with his fathers, and they buried him in Samaria: and Joas his son reigned in his stead.
Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
10 In the seven and thirtieth year of Joas king of Juda, Joas the son of Joachaz reigned over Israel in Samaria sixteen years.
A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
11 And he did that which is evil in the sight of the Lord: he departed not from all the sins of Jeroboam the son of Nabat, who made Israel to sin, but he walked in them.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
12 But the rest of the acts of Joas, and all that he did, and his valour wherewith he fought against Amasias king of Juda, are they not written in the book of the words of the days of the kings of Israel?
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
13 And Joas slept with his fathers: and Jeroboam sat upon his throne. But Joas was buried in Samaria with the kings of Israel.
Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
14 Now Eliseus was sick of the illness whereof he died: and Joas king of Israel went down to him, and wept before him, and said: O my father, my father, the chariot of Israel and the guider thereof.
To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
15 And Eliseus said to him: Bring a bow and arrows. And when he had brought him a bow, and arrows,
Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
16 He said to the king of Israel: Put thy hand upon the bow. And when he had put his hand, Eliseus put his hands over the king’s hands,
Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
17 And said: Open the window to the east. And when he had opened it, Eliseus said: Shoot an arrow. And he shot. And Eliseus said: The arrow of the Lord’s deliverance, and the arrow of the deliverance from Syria: and thou shalt strike the Syrians in Aphec, till thou consume them.
Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
18 And he said: Take the arrows. And when he had taken them, he said to him: Strike with an arrow upon the ground. And he struck three times and stood still.
Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
19 And the man of God was angry with him, and said: If thou hadst smitten five or six or seven times, thou hadst smitten Syria even to utter destruction: but now three times shalt thou smite it.
Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
20 And Eliseus died, and they buried him. And the rovers from Moab came into the land the same year.
Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
21 And some that were burying a man, saw the rovers, and cast the body into the sepulchre of Eliseus. And when it had touched the bones of Eliseus, the man came to life, and stood upon his feet.
Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
22 Now Hazael king of Syria afflicted Israel all the days of Joachaz:
Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
23 And the Lord had mercy on them, and returned to them because of his covenant, which he had made with Abraham and Isaac and Jacob: and he would not destroy them, nor utterly cast them away, unto this present time.
Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
24 And Hazael king of Syria died, and Benadad his son reigned in his stead.
Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
25 Now Joas the son of Joachaz, took the cities out of the hand of Benadad, the son of Hazael, which he had taken out of the hand of Joachaz his father by war, three times did Joas beat him, and he restored the cities to Israel.
Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.

< 2 Kings 13 >