< 2 Chronicles 32 >

1 After these things, and this truth, Sennacherib king of the Assyrians came and entered into Juda, and besieged the fenced cities, desiring to take them.
Bayan dukan abin da Hezekiya ya yi cikin aminci, sai Sennakerib sarkin Assuriya ya zo ya yaƙi Yahuda. Ya yi kwanto wa biranen katanga, yana zato zai ci su da yaƙi wa kansa.
2 And when Ezechias saw that Sennacherib was come, and that the whole force of the war was turning against Jerusalem,
Sa’ad da Hezekiya ya ga Sennakerib ya zo yana kuma niyya yă yaƙi Urushalima,
3 He took counsel with the princes, and the most valiant men, to stop up the heads of the springs, that were without the city: and as they were all of this mind,
sai ya yi shawara da fadawansa da hafsoshin mayaƙansa cewa su datse ruwa daga maɓulɓulan ruwan da yake waje da birnin, suka kuwa taimake shi.
4 He gathered together a very great multitude, and they stopped up all the springs, and the brook, that ran through the midst of the land, saying: Lest the kings of the Assyrians should come, and And abundance of water.
Sai babban taro suka haɗu suka datse dukan maɓulɓulai da rafuffukan da suke gudu cikin ƙasar. Suka ce “Me zai sa sarakunan Assuriya su zo su sami ruwa barkatai?”
5 He built up also with great diligence all the wall that had been broken down, and built towers upon it, and another wall without: and he repaired Mello in the city of David, and made all sorts of arms and shields:
Sai suka yi aiki tuƙuru suna gyaran dukan sassan katangar da suka fāɗi, suna kuma gina hasumiya a kai. Ya gina wata katanga a waje da wannan, ya kuma ƙara ƙarfin madogaran gini na Birnin Dawuda. Ya yi makamai masu yawa da kuma garkuwoyi.
6 And he appointed captains of the soldiers of the army: and he called them all together in the street of the gate of the city, and spoke to their heart, saying:
Ya naɗa manyan hafsoshi a kan mutane, ya tattara su a gabansa a fili a ƙofar birni, ya kuma ƙarfafa su da waɗannan kalmomi.
7 Behave like men, and take courage: be not afraid nor dismayed for the king of the Assyrians, nor for all the multitude that is with him: for there are many more with us than with him.
“Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro ko ku yi fargaba saboda sarkin Assuriya, da mayaƙan nan masu yawa da suke tare da shi, gama shi wanda yake tare da mu, ya fi wanda yake tare da su.
8 For with him is an arm of flesh: with us the Lord our God, who is our helper, and fighteth for us. And the people were encouraged with these words of Ezechias king of Juda.
Mayaƙa na jiki ne kawai suke tare da shi, amma Ubangiji Allahnmu ne yake tare da mu, zai kuwa taimake mu yă kuma yi yaƙinmu.” Mutane kuwa suka amince da maganar Hezekiya, Sarkin Yahuda.
9 After this, Sennacherib king of the Assyrians sent his servants to Jerusalem, (for he with all his army was besieging Lachis, ) to Ezechias king of Juda, and to all the people that were in the city, saying:
Daga baya, sa’ad da Sennakerib sarkin Assuriya da dukan mayaƙansa suke kwanto wa Lakish, sai ya aiki hafsoshinsa da wannan saƙo wa Hezekiya sarkin Yahuda da kuma wa dukan mutanen Yahuda waɗanda suke can cewa,
10 Thus saith Sennacherib king of the Assyrians: In whom do you trust, that you sit still besieged in Jerusalem?
“Ga abin da Sennakerib sarkin Assuriya ya ce ga me kake dogara, har da ka dāge cikin Urushalima da aka yi mata kwanto?
11 Doth not Ezechias deceive you, to give you up to die by hunger and thirst, affirming that the Lord your God shall deliver you from the hand of the king of the Assyrians?
Ai, Hezekiya, ruɗinku yake yi, don yă sa ku mutu da yunwa da ƙishirwa sa’ad da yake ce muku, ‘Ubangiji Allahnmu zai cece mu daga hannun sarkin Assuriya.’
12 Is it not this same Ezechias, that hath destroyed his high places, and his altars, and commanded Juda and Jerusalem, saying: You shall worship before one altar, and upon it you shall burn incense?
Hezekiya kansa bai rushe waɗannan masujadan kan tudu da bagadai, yana ce wa Yahuda da Urushalima, ‘Dole ku yi sujada a gaban bagade guda ku kuma ƙone hadayu a kansa ba’?
13 Know you not what I and my fathers have done to all the people of the lands? have the gods of any nations and lands been able to deliver their country out of my hand?
“Ba ku san abin da ni da kuma kakannina suka yi wa dukan mutanen sauran ƙasashe ba? Allolin ƙasashen nan sun taɓa iya ceton ƙasarsu daga hannuna ne?
14 Who is there among all the gods of the nations, which my fathers have destroyed, that could deliver his people out of my hand, that your God should be able to deliver you out of this hand?
Wanne a cikin dukan allolin waɗannan ƙasashe da kakannina suka hallaka ya taɓa iya ceton mutanensa daga gare ni? To, yaya Allahnku zai iya cetonku daga hannuna?
15 Therefore let not Ezechias deceive you, nor delude you with a vain persuasion, and do not believe him. For if no god of all the nations and kingdoms, could deliver his people out of my hand, and out of the hand of my fathers, consequently neither shall your God be able to deliver you out of my hand.
Yanzu fa, kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku yă kuma ɓad da ku haka. Kada ku gaskata shi, gama babu allahn wata ƙasa ko masarautar da ya taɓa iya ceton mutanensa daga hannuna ko kuwa hannun kakannina. Balle har Allahnku yă cece ku daga hannuna!”
16 And many other things did his servants speak against the Lord God, and against Ezechias his servant.
Hafsoshin Sennakerib suka ci gaba da maganar banza wa Ubangiji Allah da kuma a kan bawansa Hezekiya.
17 He wrote also letters full of blasphemy against the Lord the God of Israel, and he spoke against him: As the gods of other nations could not deliver their people out of my hand, so neither can the God of Ezechias deliver his people out of this hand.
Sarki ya kuma rubuta wasiƙu yana zagin Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana faɗin wannan a kansa, “Kamar yadda sauran allolin mutanen sauran ƙasashe ba su iya kuɓutar da mutane daga hannuna ba, haka Allahn Hezekiya ba zai kuɓutar da mutanensa daga hannuna ba.”
18 Moreover he cried out with a loud voice, in the Jews’ tongue, to the people that sat on the walls of Jerusalem, that he might frighten them, and take the city.
Sa’an nan suka yi magana da ƙarfi cikin Yahudanci wa mutanen Urushalima waɗanda suke kan katanga, don su firgita su, su kuma sa su ji tsoro don su iya cin birnin.
19 And he spoke against the God of Jerusalem, as against the gods of the people of the earth, the works of the hands of men.
Suka yi magana game da Allah na Urushalima yadda suka yi game da allolin sauran mutanen duniya, aikin hannuwan mutane.
20 And Ezechias the king, and Isaias the prophet the son of Amos, prayed against this blasphemy, and cried out to heaven.
Sarki Hezekiya da annabi Ishaya ɗan Amoz suka yi kuka cikin addu’a ga sama game da wannan.
21 And the Lord sent an angel who cut off all the stout men and the warriors, and the captains of the army of the king of the Assyrians: and he returned with disgrace into his own country. And when he was come into the house of his god, his sons that came out of his bowels, slew him with the sword.
Sai Ubangiji ya aiki mala’ika, wanda ya karkashe dukan jarumawa da shugabanni da kuma hafsoshi a sansanin sarkin Assuriyawa. Saboda haka sai sarkin Assuriya ya janye zuwa ƙasarsa da kunya. Da ya shiga haikalin Allahnsa, sai waɗansu a cikin’ya’yansa maza suka yanka shi da takobi.
22 And the Lord saved Ezechias and the inhabitants of Jerusalem, out of the hand of Sennacherib king of the Assyrians, and out of the hand of all, and gave them treasures on every side.
Ta haka Ubangiji ya ceci Hezekiya da mutanen Urushalima daga hannun Sennakerib sarkin Assuriya da kuma daga hannun dukan sauran. Ya magance su a kowane gefe.
23 Many also brought victims, and sacrifices to the Lord to Jerusalem, and presents to Ezechias king of Juda: and he was magnified thenceforth in the sight of all nations.
Yawanci mutane suka kawo hadayun ƙonawa zuwa Urushalima wa Ubangiji da kuma kyautai masu daraja wa Hezekiya sarkin Yahuda. Daga lokacin zuwa gaba dukan ƙasashe suka girmama shi.
24 In those days Ezechias was sick even to death, and he prayed to the Lord: and he heard him, and gave him a sign.
A kwanakin nan Hezekiya ya yi ciwo, ya yi kusan mutuwa. Sai ya yi addu’a ga Ubangiji, wanda ya amsa masa ya kuma ba shi alama.
25 But he did not render again according to the benefits which he had received, for his heart was lifted up: and wrath was enkindled against him, and against Juda and Jerusalem.
Amma zuciyar Hezekiya ta yi girman kai, bai kuwa yi amfani da alherin da aka nuna masa ba, saboda haka fushin Ubangiji ya sauko a kansa da kuma a kan Yahuda da Urushalima.
26 And he humbled himself afterwards, because his heart had been lifted up, both he and the inhabitants of Jerusalem: and therefore the wrath of the Lord came not upon them in the days of Ezechias.
Sai Hezekiya ya tuba daga girma kan zuciyarsa, haka ma mutanen Urushalima; saboda haka fushin Ubangiji bai zo a kansu a kwanakin Hezekiya ba.
27 And Ezechias was rich, and very glorious, and he gathered himself great treasures of silver and of gold, and of precious stones, of spices, and of arms, of all kinds, and of vessels of great price.
Hezekiya mai arziki da girma ne ƙwarai, ya kuma yi baitulmali domin azurfa da zinariyarsa da kuma domin duwatsu masu daraja, kayan yaji, garkuwoyi da kuma domin dukan kayayyaki masu daraja nasa.
28 Storehouses also of corn, of wine, and of oil, and stalls for all beasts, and folds for cattle.
Ya kuma yi gine-gine domin ajiyar hatsi, sabon ruwa inabi da mai; ya kuma yi wuraren ajiyar kowane irin shanu dabam-dabam, da kuma turke domin tumaki.
29 And he built himself cities: for he had flocks of sheep, and herds without number, for the Lord had given him very much substance.
Ya gina ƙauyuka ya kuma samo shanu da garkuna masu yawa, gama Allah ya ba shi arziki mai yawa sosai.
30 This same Ezechias was, he that stopped the upper source of the waters of Gihon, and turned them away underneath toward the west of the city of David: in ail his works he did prosperously what he would.
Hezekiya ne ya datse ruwan bisa na maɓulɓular Gihon, ya sa ruwan ya gangara zuwa gefe yamma na Birnin Dawuda. Ya yi nasara a kome da ya yi.
31 But yet in the embassy of the princes of Babylon, that were sent to him, to inquire of the wonder that had happened upon the earth, God left him that he might be tempted, and all things might be made known that were in his heart.
Amma da masu mulkin Babilon suka aika da jakadu su tambaye shi game alamar da ta faru a ƙasar, Allah ya rabu da shi don yă gwada shi don yă kuma san kome da yake cikin zuciyarsa.
32 Now the rest of the acts of Ezechias, and of his mercies are written in the book of the kings of Juda and Israel.
Sauran ayyukan mulkin Hezekiya da kuma kyawawa ayyukansa, suna a rubuce a cikin wahayin annabi Ishaya ɗan Amoz, a cikin littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
33 And Ezechias slept with his fathers, and they buried him above the sepulchres of the sons of David: and all Juda, and all the inhabitants of Jerusalem celebrated his funeral: and Manasses his son reigned in his stead.
Hezekiya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a kan tudu inda makabartan zuriyar Dawuda suke. Dukan Yahuda da kuma mutanen Urushalima suka girmama shi sa’ad da ya mutu. Sai Manasse ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 2 Chronicles 32 >