< 2 Chronicles 24 >
1 Joas was seven years old when he began to reign: and he reigned forty years in Jerusalem: the name of his mother was Sebia of Bersabee.
Yowash yana da shekara goma sha bakwai sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi sarauta a Urushalima shekara arba’in. Sunan mahaifiyarsa Zibiya ce; ita daga Beyersheba.
2 And he did that which is good before the Lord all the days of Joiada the priest.
Yowash ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji duka shekarun Yehohiyada firist.
3 And Joiada took for him two wives, by whom he had sons and daughters.
Yehohiyada ya zaɓi mata biyu dominsa, yana kuma da’ya’ya maza da’ya’ya mata.
4 After this Joas had a mind to repair the house of the Lord.
Wani lokaci daga baya Yowash ya yanke shawara yă gyara haikalin Ubangiji.
5 And he assembled the priests, and the Levites, and said to them: Go out to the cities of Juda, and gather of all Israel money to repair the temple of your God, from year to year: and do this with speed: but the Levites were negligent.
Ya tara firistoci da Lawiyawa wuri ɗaya ya ce musu, “Ku je garuruwan Yahuda ku karɓa kuɗin da ya kamata a biya shekara-shekara daga dukan Isra’ila, don gyaran haikalin Allahnku. Ku yi haka yanzu.” Amma Lawiyawa ba su yi haka nan da nan ba.
6 And the king called Joiada the chief, and said to him: Why hast thou not taken care to oblige the Levites to bring in out of Juda and Jerusalem the money that was appointed by Moses the servant of the Lord for all the multitude of Israel to bring into the tabernacle of the testimony?
Saboda haka sarki ya kira Yehohiyada babban firist ya ce masa, “Me ya sa ba ka bukaci Lawiyawa su kawo harajin da Musa bawan Ubangiji ya ce a biya daga Yahuda da Urushalima da kuma taron Isra’ila domin Tentin Sujada Shaida ba?”
7 For that wicked woman Athalia, and her children have destroyed the house of God, and adorned the temple of Baal with all the things that had been dedicated in the temple of the Lord.
Yanzu’ya’ya muguwar macen nan Ataliya maza sun fasa zuwa cikin haikalin Allah, suka kuma yi amfani da kayayyaki masu tsarki ma wa Ba’al.
8 And the king commanded, and they made a chest: and set it by the gate of the house of the Lord on the outside.
Bisa ga umarnin sarki, aka yi akwati aka sa a waje, a mashigin haikalin Ubangiji.
9 And they made a proclamation in Juda and Jerusalem, that every man should bring to the Lord the money which Moses the servant of God appointed for all Israel, in the desert.
Aka yi umarni a Yahuda da Urushalima cewa ya kamata suka kawo wa Ubangiji harajin da Musa bawan Allah ya bukaci daga Isra’ila a hamada.
10 And all the princes, and all the people rejoiced: and going In they contributed and cast so much into the chest of the Lord, that it was filled.
Dukan hafsoshi da dukan mutane suka kawo nasu kuɗin da aka sa musu da farin ciki, suna zuba su cikin akwatin sai da ya cika.
11 And when it was time to bring the chest before the king by the hands of the Levites, (for they saw there was much money, ) the king’s scribe, and he whom the high priest had appointed went in: and they poured out the money that was in the chest: and they carried back the chest to its place: and thus they did from day to day, and there was gathered an immense sum of money.
Duk sa’ad da Lawiyawa suka fito da akwatin zuwa ga hafsoshin sarki, suka kuma ga cewa akwatin yana da kuɗi mai yawa, sai magatakardan fada da hafsan babban firist su zo su juya kuɗin daga akwatin su mai da shi wurinsa. Sun riƙa yin haka kullum suka tara kuɗi mai yawa.
12 And the king and Joiada gave it to those who were over the works of the house of the Lord: but they hired with it stonecutters, and artificers of every kind of work to repair the house of the Lord: and such as wrought in iron and brass, to uphold what began to be falling.
Sarki da Yehohiyada suka ba da shi ga mutanen da suka yi aikin da ake bukata don haikalin Ubangiji. Suka ɗauki masu gini da kafintoci don su gyara haikalin Ubangiji, da kuma ma’aikatan ƙarafa da tagulla don su gyara haikalin.
13 And the workmen were diligent, and the breach of the walls was closed up by their hands, and they set up the house of the Lord in its former state, and made it stand firm.
Mutanen da suke lura da aikin natsattsu ne, kuma gyare-gyaren suka ci gaba a ƙarƙashinsu. Suka sāke gina haikalin Allah bisa ga ainihin fasalinsa suka ƙara masa ƙarfi.
14 And when they had finished all the works, they brought the rest of the money before the king and Joiada: and with it were made vessels for the temple for the ministry, and for holocausts and bowls, and other vessels of gold and silver: and holocausts were offered in the house of the Lord continually all the days of Joiada.
Da suka gama, suka kawo sauran kuɗin wa sarki da Yehohiyada, da su ne kuwa aka yi kayayyaki domin hidima da kuma domin hadayun ƙonawa, haka kuma kwanoni da sauran kayayyakin zinariya da azurfa. Muddin Yehohiyada yana raye, aka riƙa kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
15 But Joiada grew old and was full of days, and died when he was a hundred and thirty years old.
Yanzu Yehohiyada ya tsufa kuma cike da shekaru, ya kuwa mutu yana da shekara ɗari da talatin.
16 And they buried him in the city of David among the kings, because he had done good to Israel, and to his house.
Aka binne shi tare da sarakuna a cikin Birnin Dawuda, saboda kirkin da ya yi a Isra’ila wa Allah da haikalinsa.
17 And after the death of Joiada, the princes of Juda went in, and worshipped the king: and he was soothed by their services and hearkened to them.
Bayan mutuwar Yehohiyada, hafsoshin Yahuda suka zo suka yi mubaya’a wa sarki, ya kuma saurare su.
18 And they forsook the temple of the Lord the God of their fathers, and served groves and idols, and wrath came upon Juda and Jerusalem for this sin.
Suka yashe haikalin Ubangiji Allah na kakanninsu, suka bauta wa ginshiƙan Ashera da kuma gumaka. Saboda laifinsu, fushin Allah ya sauko a kan Yahuda da Urushalima.
19 And he sent prophets to them to bring them back to the Lord, and they would not give ear when they testified against them.
Ko da yake Ubangiji ya aiki annabawa zuwa wurin mutane don su dawo da su gare shi, kuma ko da yake sun ba da shaida a kansu, ba su saurara ba.
20 The spirit of God then came upon Zacharias the son of Joiada the priest, and he stood in the sight of the people, and said to them: Thus saith the Lord God: Why transgress you the commandment of the Lord which will not be for your good, and have forsaken the Lord, to make him forsake you?
Sai Ruhun Allah ya sauko a kan Zakariya ɗan Yehohiyada firist. Ya tsaya a gaban mutane ya ce, “Ga abin da Allah ya ce, ‘Me ya sa ba ku yi biyayya da umarnan Ubangiji ba? Ba za ku yi nasara ba. Domin kun yashe Ubangiji, shi ma ya yashe ku.’”
21 And they gathered themselves together against him, and stoned him at the king’s commandment in the court of the house of the Lord.
Amma suka yi masa maƙarƙashiya, kuma ta wurin umarnin sarki suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu a filin haikalin Ubangiji.
22 And king Joas did not remember the kindness that Joiada his father had done to him, but killed his son. And when he died, he said: The Lord see, and require it.
Sarki Yowash bai tuna da alherin da Yehohiyada mahaifin Zakariya ya nuna masa ba, sai ya kashe ɗansa, wanda ya ce yayinda yake mutuwa, “Bari Ubangiji yă dubi wannan yă kuma sāka maka.”
23 And when a year was come about, the army of Syria came up against him: and they came to Juda and Jerusalem, and killed all the princes of the people, and they sent all the spoils to the king of Damascus.
Da shekara ta kewaye, mayaƙan Aram suka yi gāba da Yowash suka kai hari wa Yahuda da Urushalima suka kuma kashe dukan shugabannin mutane, suka aika da dukan ganima zuwa ga sarkinsu a Damaskus.
24 And whereas there came a very small number of the Syrians, the Lord delivered into their hands an infinite multitude, because they had forsaken the Lord the God of their fathers: and on Joas they executed shameful judgments.
Ko da yake mayaƙan Arameyawa sun zo da mutane kaɗan kawai, Ubangiji ya sa suka ci nasara a kan sojojin Yahuda mafi yawa, don mutanen Yahuda sun rabu da Ubangiji Allah na kakanninsu, aka kuma hukunta Yowash.
25 And departing they left him in diseases: and his servants rose up him, for revenge of the blood of the son of Joiada the priest, and they slew him in his bed, and he died: and they buried him in the city of David, but not in the sepulchres of the kings.
Sa’ad da Arameyawa suka janye, suka bar Yowash da mummunan rauni. Hafsoshinsa suka haɗa baki a kansa saboda kisan ɗan Yehohiyada firist da ya yi, suka kashe shi a kan gadonsa. Ta haka ya mutu aka kuma binne shi makabartan sarakuna.
26 Now the men that conspired against him were Zabad the son of Semmaath an Ammonitess, and Jozabad the son of Semarith a Moabitess.
Waɗanda suka haɗa bakin kuwa su ne Zabad ɗan Shimeyat wata mutuniyar Ammon da Yehozabad ɗan Shimrit wata mutuniyar Mowab.
27 And concerning his sons, and the sum of money which was gathered under him, and the repairing the house of God; they are written more diligently in the book of kings: and Amasias his son reigned in his stead.
Labarin’ya’yansa maza, annabce-annabce masu yawa game da shi, da tarihin gyaran haikalin Allah suna a rubuce a rubuce-rubuce a littafin sarakuna. Amaziya ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.