< 2 Chronicles 19 >
1 And Josaphat king of Juda returned to his house in peace to Jerusalem.
Sa’ad da Yehoshafat sarkin Yahuda ya dawo zuwa fadansa a Urushalima lafiya,
2 And Jehu the son of Hanani the seer met him, and said to him: Thou helpest the ungodly, and thou art joined in friendship with them that hate the Lord, and therefore thou didst deserve indeed the wrath of the Lord:
Yehu mai duba, ɗan Hanani, ya fita don yă tarye shi, ya kuma ce wa sarki, “Ya yi kyau ke nan da ka taimaki mugu ka kuma ƙaunaci waɗanda suke ƙin Ubangiji? Da yake ka yi haka fushin Ubangiji yana a kanka
3 But good works are found in thee, because thou hast taken away the groves out of the land of Juda, and hast prepared thy heart to seek the Lord the God of thy fathers.
Duk da haka an sami wani abin kirki a wurinka, gama ka kawar da ginshiƙan Ashera a ƙasar, ka kuma sa zuciyarka a kan neman Allah.”
4 And Josaphat dwelt at Jerusalem: and he went out again to the people from Bersabee to mount Ephraim, and brought them back to the Lord the God of their fathers.
Yehoshafat ya zauna a Urushalima, ya kuma fita yana shiga cikin mutane daga Beyersheba zuwa ƙasar tudun Efraim ya kuma juyar da su ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
5 And he set judges of the land in all the fenced cities of Juda, in every place.
Ya naɗa alƙalai a kowanne daga cikin biranen katanga na Yahuda a ƙasar.
6 And charging the judges, he said: Take heed what you do: for you exercise not the judgment of man, but of the Lord: and whatsoever you judge, it shall redound to you.
Ya faɗa musu, “Ku lura da abin da kuke yi, gama shari’ar da kuke yi ba ta mutum ba ce, amma ta Ubangiji ce, yana tare da ku sa’ad da kuke yanke shari’a.
7 Let the fear of the Lord be with you, and do all things with diligence: for there is no iniquity with the Lord our God, a nor respect of persons, nor desire of gifts.
Yanzu fa ku ji tsoron Ubangiji. Ku yi hankali a kan abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu ba ya sonkai ko nuna wariya ko cin hanci.”
8 In Jerusalem also Josaphat appointed Levites, and priests and chiefs of the families of Israel, to judge the judgment and the cause of the Lord for the inhabitants thereof.
A Urushalima kuma, Yehoshafat ya naɗa waɗansu Lawiyawa, firistoci da kawunan iyalan Isra’ilawa don su tabbatar da an bi dokar Ubangiji, su kuma sasanta tsakanin mutane. A Urushalima za su zauna.
9 And he charged them, saying: Thus shall you do in the fear of the Lord faithfully, and with a perfect heart.
Ya ba su waɗannan umarnai, “Ku yi aikinku da aminci da tsoron Ubangiji da dukan zuciyarku.
10 Every cause that shall come to you of your brethren, that dwell in their cities, between kindred and kindred, wheresoever there is question concerning the law, the commandment, the ceremonies, the justifications: shew it them, that they may not sin against the Lord, and that wrath may not come upon you and your brethren: and so doing you shall not sin.
Cikin kowane batun da ya zo gabanku daga’yan’uwanku waɗanda suke zama a birane, ko batun na kisa ne ko kuwa waɗansu batuttuwan da suka shafi doka, umarnai, ƙa’idodi ko farillai, dole ku ja musu kunne kada su yi wa Ubangiji zunubi; in ba haka ba fushinsa zai sauko a kanku da’yan’uwanku. Ku yi wannan, ta haka ba za ku kuwa yi zunubi ba.
11 And Amarias the priest your high priest shell be chief in the things which regard God: and Zabadias the son of Ismahel, who is ruler in the house of Juda, shall be over those matters which belong to the king’s office: and you have before you the Levites for masters, take courage and do diligently, and the Lord will be with you in good things.
“Amariya, babban firist, shi ne zai shugabance ku a kan dukan al’amuran da suke na wajen Ubangiji, Zebadiya ɗan Ishmayel kuwa, shugabanku a kan dukan al’amuran da suka shafi sarki, Lawiyawa kuma za su zama a matsayin manya a gabanku. Ku yi abubuwa da ƙarfin hali, bari kuma Ubangiji yă kasance tare da masu yin gaskiya.”