< 1 Samuel 16 >

1 And the Lord said to Samuel. How It long wilt thou mourn for Saul, whom I have rejected from reigning over Israel? fill thy horn with oil, and come, that I may send thee to Isai the Bethlehemite: for I have provided me a king among his sons.
Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Har yaushe za ka yi ta makoki saboda Shawulu? Na riga na ƙi shi da zaman sarkin Isra’ila. Ka cika ƙahonka da mai, zan aike ka zuwa wurin Yesse na Betlehem. Na zaɓi ɗaya daga cikin’ya’yansa maza yă zama sarki.”
2 And Samuel said: How shall I go? for Saul will hear of it, and he will kill me. And the Lord said: Thou shalt take with thee a calf of the herd, and thou shalt say: I am come to sacrifice to the Lord.
Amma Sama’ila ya ce, “Yaya zan yi haka? Ai, in Shawulu ya ji labari, zai kashe ni.” Ubangiji ya ce, “To, sai ka tafi tare da’yar karsana ka ce, ‘Na zo don in yi wa Ubangiji hadaya.’
3 And thou shalt call Isai to the sacrifice, and I will shew thee what thou art to do, and thou shalt anoint him whom I shall shew to thee.
Ka gayyato Yesse a wurin hadayar, ni kuma zan gaya maka abin da za ka yi. Za ka shafe mini wanda na nuna maka.”
4 Then Samuel did as the Lord had said to him. And he came to Bethlehem, and the ancients of the city wondered, and meeting him, they said: Is thy coming hither peaceable?
Sama’ila kuwa ya yi abin da Ubangiji ya umarce shi. Da ya isa Betlehem, sai dattawan garin suka tarye shi da rawar jiki, suka ce masa, “Mai duba, wannan ziyara lafiya dai ko?”
5 And he said: It is peaceable: I am come to offer sacrifice to the Lord, be ye sanctified, and come with me to the sacrifice. And he sanctified Isai and his sons, and called them to the sacrifice.
Sama’ila ya ce, “I, lafiya ƙalau. Na zo ne domin in yi wa Ubangiji hadaya. Ku tsarkake kanku sa’an nan ku zo mu tafi wurin yin hadaya tare.” Ya kuma sa Yesse da’ya’yansa maza su tsarkake kansu, su je wurin hadayar.
6 And when they were come in, he saw Eliab, and said: Is the Lord’s anointed before him?
Da isarsu, Sama’ila ya ga Eliyab sai ya yi tsammani shi ne, sai ya ce, “Lalle ga shafaffe na Ubangiji tsaye a gaban Ubangiji.”
7 And the Lord said to Samuel: Look not on his countenance, nor on the height of his stature: because I have rejected him, nor do I judge according to the look of man: for man seeth those things that appear, but the Lord beholdeth the heart.
Amma Ubangiji ya ce wa Sama’ila, “Kada ka dubi kyan tsarinsa ko tsayinsa, domin ba shi nake so ba, gama yadda Ubangiji yake gani, ba haka mutum yake gani ba. Mutum yakan dubi kyan tsari ne kawai daga waje, amma Ubangiji yakan dubi zuciya.”
8 And Isai called Abinadab, and brought him before Samuel. And he said: Neither hath the Lord chosen this.
Sai Yesse ya kira Abinadab yă zo gaban Sama’ila. Amma Sama’ila ya ce, “Ko wannan ma Ubangiji bai zaɓe shi ba.”
9 And Isai brought Samma, and he said of him: Neither hath the Lord chosen this.
Sai Yesse ya sa Shamma yă zo gaban Sama’ila, amma Sama’ila ya ce, “Ubangiji bai zaɓi wannan ma ba.”
10 Isai therefore brought his seven sons before Samuel: and Samuel said to Isai: The Lord hath not chosen any one of these.
Yesse ya sa’ya’yansa maza bakwai suka wuce gaban Sama’ila, amma Sama’ila ya ce masa, “Ubangiji bai zaɓi waɗannan ba.”
11 And Samuel said to Isai: Are here all thy sons? He answered: There remaineth yet a young one, who keepeth the sheep. And Samuel said to Isai: Send, and fetch him, for we will not sit down till he come hither.
Don haka ya tambayi Yesse ya ce, “Su ke nan’ya’yan maza da kake da su?” Yesse ya ce, “Har yanzu akwai ɗan autan, amma yana kiwon tumaki.” Sama’ila ya ce, “Ka aika yă zo, ba za mu zauna ba sai ya iso.”
12 He sent therefore and brought him Now he was ruddy and beautiful to behold, and of a comely face. And the Lord said: Arise, and anoint him, for this is he.
Sai ya aika aka kawo shi. Ga shi kuwa kyakkyawan saurayi ne mai kyan gani. Ubangiji ya ce, “Tashi ka shafe shi, shi ne wannan.”
13 Then Samuel took the horn of oil, and anointed him in the midst of his brethren: and the spirit of the Lord came upon David from that day forward: and Samuel rose up, and went to Ramatha.
Saboda haka Sama’ila ya ɗauko ƙahon nan da yake da mai ya shafe Dawuda a gaban’yan’uwansa. Daga wannan rana kuwa ruhun Ubangiji ya sauko wa Dawuda da iko. Sai Sama’ila ya koma Rama.
14 But the spirit of the Lord departed from Saul, and an evil spirit from the Lord troubled him.
To, fa, Ruhun Ubangiji ya riga ya rabu da Shawulu, sai mugun ruhu daga Ubangiji ya soma ba shi wahala.
15 And the servants of Saul said to him: Behold now an evil spirit from God troubleth thee.
Ma’aikatan Shawulu suka ce masa, “Duba, ga mugun ruhu daga Allah yana ba ka wahala.
16 Let our lord give orders, and thy servants who are before thee will seek out a man skillful in playing on the harp, that when the evil spirit from the Lord is upon thee, he may play with his hand, and thou mayest bear it more easily.
Ranka yă daɗe, muna so ka ba mu izini mu tafi, mu nemo wanda ya iya kiɗan molo, domin duk sa’ad da mugun ruhun nan daga Allah ya tashi, sai yă kaɗa molon don hankalinka yă kwanta.”
17 And Saul said to his servants: Provide me then some man that can play well, and bring him to me.
Saboda haka Shawulu ya ce wa ma’aikatansa, “Ku nemo wanda ya iya kiɗan molo sosai ku kawo mini.”
18 And one of the servants answering, said: Behold I have seen a son of Isai the Bethlehemite, a skillful player, and one of great strength, and a man fit for war, and prudent in his words, and a comely person: and the Lord is with him.
Ɗaya daga cikin bayin ya ce, “Na san wani yaro, ɗan Yesse na Betlehem, ya iya kiɗan molo, yana da hikima, shi kuma ya iya yaƙi. Ya iya magana, ga shi kuma kyakkyawa, Ubangiji kuwa yana tare da shi.”
19 Then Saul sent messengers to Isai, saying: Send me David thy son, who is in the pastures.
Sai Shawulu ya aiki manzanni zuwa wurin Yesse ya ce, “Ka aiko mini da ɗanka Dawuda wanda yake kiwon tumaki.”
20 And Isai took an ass laden with bread, and a bottle of wine, and a kid of the flock, and sent them by the hand of David his son to Saul.
Saboda haka Yesse ya ɗauki jaki tare da burodi da ruwan inabi da ɗan ƙarami bunsuru ya ba wa ɗansa Dawuda yă kai wa Shawulu.
21 And David came to Saul, and stood before him: and he loved him exceedingly, and made him his armourbearer.
Dawuda ya isa wurin Shawulu ya shiga hidimarsa. Shawulu kuwa ya so shi ƙwarai da gaske. Dawuda ya zama ɗaya daga cikin masu sanya sulke.
22 And Saul sent to Isai, saying: Let David stand before me: for he hath found favour in my sight.
Sa’an nan Shawulu ya aika saƙo wurin Yesse cewa, “Ka bar Dawuda yă yi mini hidima domin ina jin daɗinsa ƙwarai.”
23 So whensoever the evil spirit from the Lord was upon Saul, David took his harp, and played with his hand, and Saul was refreshed, and was better, for the evil spirit departed from him.
Duk lokacin da ruhun nan daga Allah ya sauko a kan Shawulu, sai Dawuda yă ɗauki molonsa yă kaɗa. Sa’an nan sauƙi yă zo wa Shawulu, mugun ruhu kuma yă rabu da shi.

< 1 Samuel 16 >