< 1 Kings 11 >
1 And king Solomon loved many strange women besides the daughter of Pharao, and women of Moab, and of Ammon, and of Edom, and of Sidon, and of the Hethites:
Sarki Solomon ya ƙaunaci baƙin mata. Ban da’yar Fir’auna, ya auri Mowabawa, Ammonawa, mutanen Edom, Sidoniyawa da Hittiyawa.
2 Of the nations concerning which the Lord said to the children of Israel: You shall not go in unto them, neither shall any of them come in to yours: for they will most certainly turn away your heart to follow their gods. And to these was Solomon joined with a most ardent love.
Sun fito daga al’ummai da Ubangiji ya ce wa Isra’ilawa, “Kada ku yi aurayya da su, domin tabbatacce za su juye zukatanku zuwa ga waɗansu alloli.” Duk da haka Solomon ya manne musu, ya nace, yana ƙaunarsu.
3 And he had seven hundred wives as queens, and three hundred concubines: and the women turned away his heart.
Ya auri mata ɗari bakwai, haifaffun gidan sarauta, da kuma ƙwarƙwarai ɗari uku. Matan nan nasa suka karkatar da shi.
4 And when he was now old, his heart was turned away by women to follow strange gods: and his heart was not perfect with the Lord his God, as was the heart of David his father.
Yayinda Solomon yake tsufa, matansa suka juye zuciyarsa ga bin waɗansu alloli, zuciyarsa kuwa ba tă bi Ubangiji Allahnsa ɗungum kamar yadda zuciyar Dawuda mahaifinsa ta kasance ba.
5 But Solomon worshipped Astarthe the goddess of the Sidonians, and Moloch the idol of the ammonites.
Ya bi Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
6 And Solomon did that which was net pleasing before the Lord, and did not fully follow the Lord, as David his father.
Saboda haka Solomon ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji. Bai bi Ubangiji gaba ɗaya kamar yadda Dawuda mahaifinsa ya yi ba.
7 Then Solomon built a temple for Chamos the idol of Moab, on the hill that is over against Jerusalem, and for Moloch the idol of the children of Ammon.
A kan tudu, gabas da Urushalima, Solomon ya gina masujada a can domin Kemosh, allahn da aka hana na Mowab, da Molek, allahn da aka hana na Ammonawa.
8 And he did in this manner for all his wives that were strangers, who burnt incense, and offered sacrifice to their gods.
Ya yi haka domin dukan baƙin matansa, waɗanda suka ƙone turare suka kuma miƙa hadayu ga allolinsu.
9 And the Lord was angry with Solomon, because his mind was turned away from the Lord the God of Israel, who had appeared to him twice,
Ubangiji ya yi fushi da Solomon domin zuciyarsa ya juye daga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda ya bayyana masa sau biyu.
10 And had commanded him concerning this thing, that he should not follow strange gods: but he kept not the things which the Lord commanded him.
Ko da yake ya hana Solomon bin waɗansu alloli, Solomon bai kiyaye umarnin Ubangiji ba.
11 The Lord therefore said to Solomon: Because thou hast done this, and hast not kept my covenant, and my precepts, which I have commanded thee, I will divide and rend thy kingdom, and will give it to thy servant.
Saboda haka Ubangiji ya ce wa Solomon, “Da yake halinka ke nan, ba ka kuma kiyaye alkawarina, da ƙa’idodina da na umarce ka ba, tabbatacce zan yage masarautar daga gare ka, in ba da ita ga ɗaya daga cikin bayinka.
12 Nevertheless in thy days I will not do it, for David thy father’s sake: but I will rend it out of the hand of thy son.
Amma saboda Dawuda mahaifinka, ba zan yi haka a zamaninka ba. Zan yage ta daga hannun ɗanka.
13 Neither will I take away the whole kingdom, but I will give one tribe to thy son for the sake of David my servant, and Jerusalem which I have chosen.
Amma ba zan yage dukan masarautar daga gare shi ba, zan ba shi kabila ɗaya saboda Dawuda bawana, da kuma saboda Urushalima, wadda na zaɓa.”
14 And the Lord raised up an adversary to Solomon, Adad the Edomite of the king’s seed, in Edom.
Sai Ubangiji ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Hadad, mutumin Edom daga gidan sarautar Edom.
15 For when David was in Edom, and Joab the general of the army was gone up to bury them that were slain, and had killed every male in Edom,
A shekarun baya Dawuda ya ci Edom da yaƙi. Yowab, shugaban sojojinsa ya tafi can domin yă binne Isra’ilawa waɗanda suka mutu a yaƙi. Sa’ad da suke a can, sojojin Isra’ila suka kashe kowane ɗa namiji a Edom.
16 (For Joab remained there six months with all Israel, till he had slain every male in Edom, )
Yowab da dukan Isra’ilawa suka zauna a can, wata shida, sai da suka hallaka dukan mutane a Edom.
17 Then Adad fled, he and certain Edomites, of his father’s servants with him, to go into Egypt: and Adad was then a little boy.
Amma Hadad yana ɗan yaro a lokaci, wanda ya gudu zuwa Masar tare da shugabannin mutanen Edom waɗanda suka yi wa mahaifinsa hidima.
18 And they arose out of Madian, and came into Pharan, and they took men with them from Pharan, and went into Egypt to Pharao the king of Egypt: who gave him a house, and appointed him victuals, and assigned him land.
Suka taso daga Midiyan suka tafi Faran. Sa’an nan suka ɗauki mutane daga Faran suka tafi Masar, zuwa wurin Fir’auna wanda ya ba wa Hadad gida da ƙasa, ya kuma tanada masa da abinci.
19 And Adad found great favour before Pharao, insomuch that he gave him to wife, the own sister of his wife Taphnes the queen.
Fir’auna ya ji daɗin Hadad har ya ba shi’yar’uwar matarsa, Sarauniya Tafenes, aure.
20 And the sister of Taphnes bore him his son Genubath, and Taphnes brought him up in the house of Pharao: and Genubath dwelt with Pharao among his children.
’Yar’uwar Tafenes ta haifi masa ɗa wanda ya kira Genubat, wanda Tafenes ta yi renonsa a fadan sarki. A can, Genubat ya yi zama da’ya’yan Fir’auna.
21 And when Adad heard in Egypt that David slept with his fathers, and that Joab the general of the army was dead, he said to Pharao: Let me depart, that I may go to my own country.
Yayinda yake a Masar, Hadad ya ji Dawuda ya huta tare da kakanninsa, ya kuma ji cewa Yowab shugaban mayaƙa ya mutu. Sai Hadad ya ce wa Fir’auna, “Bari in tafi, don in koma ƙasata.”
22 And Pharao said to him: Why, what is wanting to thee with me, that thou seekest to go to thy own country? But he answered: Nothing: yet I beseech thee to let me go.
Fir’auna ya tambaye shi, ya ce, “Me ka rasa a nan da kake so ka koma garinka?” Ya ce, “Ba kome, amma ka dai bar ni in tafi!”
23 God also raised up against him an adversary, Razon the son of Eliada, who had fled from his master Adarezer the king of Soba:
Allah kuwa ya tayar wa Solomon wani abokin gāba, mai suna Rezon, ɗan Eliyada, wanda ya gudu daga maigidansa, Hadadezer sarkin Zoba.
24 And he gathered men against him, and he became a captain of robbers, when David slew them of Soba: and they went to Damascus, and dwelt there, and they made him king in Damascus.
Rezon ya tattara mutane kewaye da shi, ya zama kuma shugaban’yan tawaye sa’ad da Dawuda ya hallaka mayaƙan Zoba;’yan tawayen suka tafi Damaskus, inda suka zauna, suka kuma yi mulki.
25 And he was an adversary to Israel, all the days of Solomon: and this is the evil of Adad, and his hatred against Israel, and he reigned in Syria.
Rezon ya zama babban abokin gāban Isra’ila cikin dukan kwanakin mulkin Solomon. Ya ƙara rikici a kan rikicin Hadad. Rezon ya ƙi mulkin Isra’ila da dukan ransa. Saboda haka Rezon ya yi mulki a Aram ya kuma ƙi jinin Isra’ila.
26 Jeroboam also the son of Nabat an Ephrathite of Sareda, a servant of Solomon, whose mother was named Sarua, a widow woman, lifted up his hand against the king.
Haka ma Yerobowam, ɗan Nebat, shi ma ya yi wa sarki tawaye. Shi ɗaya ne daga shugabannin Solomon, shi mutumin Efraim ne daga Zereda, mahaifiyarsa kuwa gwauruwa ce, mai suna Zeruwa.
27 And this is the cause of his rebellion against him, for Solomon built Mello, and filled up the breach of the city of David his father.
Ga yadda ya tayar wa sarki Solomon. Sarki Solomon ya gina madogaran gini, ya ciccika wurare a katangar birnin Dawuda mahaifinsa da ƙasa.
28 And Jeroboam was a valiant and mighty man: and Solomon seeing him a young man ingenious and industrious, made him chief over the tributes of all the house of Joseph.
To, Yerobowam mutum ne mai fasaha. Sa’ad da Solomon ya ga yadda matashin yake aiki da himma, sai ya sa shi yă lura da dukan aikin gandu na gidan Yusuf.
29 So it came to paste at that time, that Jeroboam went out of Jerusalem, and the prophet Ahias the Silonite, clad with a new garment, found him in the way: and they two were alone in the held.
Da Yerobowam ya fita Urushalima, sai annabi Ahiya, mutumin Shilo ya tarar da shi a hanya. Lokacin kuwa Ahiya yana saye da sabuwar riga, ba kowa a filin sai su biyu kaɗai.
30 And Ahias taking his new garment, wherewith he was clad, divided it into twelve parts:
Sai Ahiya ya kama sabuwar rigar da yake saye da ita ya yage ta gida goma sha biyu.
31 And he said to Jeroboam: Take to thee ten pieces: for thus saith the Lord the God of Israel: Behold I will rend the kingdom out of the hand of Solomon, and will give thee ten tribes.
Sa’an nan ya ce wa Yerobowam, “Ɗauki gida goma wa kanka, gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce ke nan, ‘Duba, zan yage masarauta daga hannun Solomon in ba ka kabilu goma.
32 But one tribe shall remain to him for the sake of my servant David, and Jerusalem the city, which I have chosen out of all the tribes of Israel:
Amma saboda bawana Dawuda da kuma birnin Urushalima, wadda na zaɓa daga dukan kabilan Isra’ila, zai sami kabila guda.
33 Because he hath forsaken me, and hath adored Astarthe the goddess of the Sidonians, and Chamos the god of Moab, and Moloch the god of the children of Ammon: and hath not walked in my ways, to do justice before me, and to keep my precepts, and judgments as did David his father.
Zan yi wannan domin sun yashe ni, suka kuma yi wa Ashtarot, alliyar Sidoniyawa, da Kemosh, allahn Mowabawa, da kuma Molek, allahn Ammonawa sujada, ba su yi tafiya a hanyoyina ba, ba su kuwa yi abin da yake daidai a idanuna ba, ba su kiyaye farillaina da dokokina kamar yadda Dawuda, mahaifin Solomon ya yi ba.
34 Yet I will not take away all the kingdom out of his hand, but I will make him prince all the days of his life, for David my servant’s sake, whom I chose, who kept my commandments and my precepts.
“‘Amma ba zan ɗauki dukan masarautar daga hannun Solomon ba; na naɗa shi sarki, dukan kwanaki ransa saboda Dawuda bawana, wanda na zaɓa, wanda kuma ya kiyaye umarnai da farillaina.
35 But I will take away the kingdom out of his son’s hand and will give thee ten tribes:
Zan ɗauke masarautar daga hannuwan ɗansa ne, in ba ka kabilu goma.
36 And to his son I will give one tribe, that there may remain a lamp for my servant David before me always in Jerusalem the city which I have chosen, that my name might be there.
Zan ba da ɗaya ga ɗansa don kullum Dawuda bawana yă kasance da fitila a gabana a Urushalima, birnin da na zaɓa in sa Sunana.
37 And I will take thee, and thou shalt reign over all that thy soul desireth, and thou shalt be king over Israel.
Amma fa, ga kai, zan ɗauke ka, za ka kuwa yi mulki bisa dukan abin da zuciyarka take so; za ka zama sarki a bisa Isra’ila.
38 If then thou wilt hearken to all that I shall command thee, and wilt walk in my ways, and do what is right before me, keeping my commandments and my precepts, as David my servant did: I will be with thee, and will build thee up a faithful house, as I built a house for David, and I will deliver Israel to thee:
In ka aikata dukan abin da na umarce ka, ka yi tafiya a hanyoyina, ka kuma yi abin da yake daidai a idanuna ta wurin kiyaye farillaina da umarnaina, kamar yadda Dawuda bawana ya yi, zan kasance tare da kai. Zan gina maka masarauta mai dawwama kamar wadda na gina wa Dawuda, zan kuma ba da Isra’ila gare ka.
39 And I will for this afflict the seed of David, but yet not for ever.
Zan ƙasƙantar da zuriyar Dawuda saboda wannan, amma ba har abada ba.’”
40 Solomon therefore sought to kill Jeroboam: but he arose, and fled into Egypt to Sesac the king of Egypt, and was in Egypt till the death of Solomon.
Solomon ya yi ƙoƙari yă kashe Yerobowam, amma Yerobowam ya tsere zuwa Masar, zuwa wurin sarki Shishak, ya zauna a can sai bayan mutuwar Solomon.
41 And the rest of the words of Solomon, and all that he did, and his wisdom: behold they are all written in the book of the words of the days of Solomon.
Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, da dukan abubuwan da ya yi, da hikimar da ya nuna, an rubuta su a littafin tarihin Solomon.
42 And the days that Solomon reigned in Jerusalem over all Israel, were forty years.
Solomon ya yi mulki a Urushalima, a bisa dukan Isra’ila, shekaru arba’in.
43 And Solomon slept with his fathers, and was buried in the city of David his father, and Roboam his son reigned in his stead.
Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a birnin Dawuda mahaifinsa. Sai Rehobowam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.