< 1 Chronicles 22 >

1 Then David said: This is the house of God, and this is the altar for the holocaust of Israel.
Sai Dawuda ya ce, “Gidan Ubangiji Allah zai kasance a nan, haka kuma bagaden hadaya ta ƙonawa don Isra’ila.”
2 And he commanded to gather together all the proselytes of the land of Israel, and out of them he appointed stonecutters to hew stones and polish them, to build the house of God.
Dawuda kuwa ya umarta a tattara baƙin da suke zama a Isra’ila, daga cikinsu ya sa masu farfasa duwatsu don su shirya duwatsun da aka sassaƙa saboda ginin gidan Allah.
3 And David prepared in abundance iron for the nails of the gates, and for the closures and joinings: and of brass an immense weight.
Ya tanada ƙarfe mai yawa don ƙusoshi saboda ƙyamaren hanyoyin shiga da kuma saboda mahaɗai, da ƙarin tagulla fiye da ƙirge.
4 And the cedar trees were without number, which the Sidonians, and Tyrians brought to David.
Ya kuma tanada gumaguman al’ul masu yawa fiye da ƙirge, gama Sidoniyawa da mutanen Taya sun kawo su wa Dawuda da yawa.
5 And David said: Solomon my son is very young and tender, and the house which I would have to be built to the Lord, must be such as to be renowned in all countries: therefore I will prepare him necessaries. And therefore before his death he prepared all the charges.
Dawuda ya ce, “Ɗana Solomon matashi ne kuma bai gogu ba, kuma gidan da za a gina wa Ubangiji zai zama mai ƙayatarwa ƙwarai, sananne da kuma mai daraja a idon dukan al’ummai. Saboda haka zan yi shirye-shirye saboda shi.” Sai Dawuda ya yi ɗumbun shirye-shirye kafin mutuwarsa.
6 And he called for Solomon his son: and commanded him to build a house to the Lord the God of Israel.
Sa’an nan ya kira ɗansa Solomon ya umarce shi yă gina gida domin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
7 And David said to Solomon: My son, it was my desire to have built a house to the name of the Lord my God.
Dawuda ya ce wa Solomon, “Ɗana, na yi niyya a zuciyata in gina gida saboda Sunan Ubangiji Allahna.
8 But the word of the Lord came to me, saying: Thou hast shed much blood, and fought many battles, so thou canst not build a house to my name, after shedding so much blood before me:
Amma wannan maganar Ubangiji ta zo mini, ‘Ka zub da jini mai yawa ka kuma yi yaƙe-yaƙe masu yawa. Ba za ka gina gida domin Sunana ba, domin ka zub da jini da yawa a duniya a idona.
9 The son, that shall be born to thee, shall be a most quiet man: for I will make him rest from all his enemies round about: and therefore he shall be called Peaceable: and I will give peace and quietness to Israel all his days.
Amma za ka haifi ɗa wanda zai zama mutumin salama da kuma hutu, zan kuma ba shi hutu daga dukan abokan gābansa a kowane gefe. Za a kira shi Solomon, zai kuma kawo wa Isra’ila salama da natsuwa a zamanin mulkinsa.
10 He shall build a house to my name, and he shall be a son to me, and I will be a father to him: and I will establish the throne of his kingdom over Israel for ever.
Shi ne wanda zai gina gida saboda Sunana. Zai zama ɗana, ni kuma zan zama mahaifinsa. Zan kafa kujerar sarautarsa a bisa Isra’ila har abada.’
11 Now then, my son, the Lord be with thee, and do thou prosper, and build the house to the Lord thy God, as he hath spoken of thee.
“Yanzu, ɗana, Ubangiji ya kasance tare da kai, bari kuma ka yi nasara ka kuma gina gidan Ubangiji Allahnka, kamar yadda ya ce za ka yi.
12 The Lord also give thee wisdom and understanding, that thou mayest be able to rule Israel, and to keep the law of the Lord thy God.
Bari Ubangiji ya ba ka basira da fahimi sa’ad da ya sa ka shugaba a bisa Isra’ila, saboda ka kiyaye dokar Ubangiji Allahnka.
13 For then thou shalt be able to prosper, if thou keep the commandments, and judgments, which the Lord commanded Moses to teach Israel: take courage and act manfully, fear not, nor be dismayed.
Ta haka za ka yi nasara in ka mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa saboda Isra’ila. Ka yi ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa. Kada ka ji tsoro ko ka fid da zuciya.
14 Behold I in my poverty have prepared the charges of the house of the Lord, of gold a hundred thousand talents, and of silver a million of talents: but of brass, and of iron there is no weight, for the abundance surpasseth all account: timber also and stones I have prepared for all the charges.
“Na sha wahala da yawa don in yi tanadi talentin dubu ɗari na zinariya, talenti miliyon na azurfa, ɗumbun tagulla da ƙarfe da suka wuce ƙirge da katako da dutse saboda haikalin Ubangiji. Za ka iya ƙara su.
15 Thou hast also workmen in abundance, hewers of stones, and masons, and carpenters, and of all trades the most skillful in their work,
Kana da ma’aikata masu yawa, masu fafarshe duwatsu, masu gini da masu aikin katako, da kuma gwanaye a kowane irin aikin
16 In gold, and in silver, and in brass, and in iron, whereof there is no number. Arise then, and be doing, and the Lord will be with thee.
zinariya da azurfa, tagulla da ƙarfe, masu sana’a waɗanda suka wuce ƙirge. Yanzu ka fara aiki, Ubangiji kuma ya kasance tare da kai.”
17 David also charged all the princes of Israel, to help Solomon his son,
Sai Dawuda ya umarta dukan shugabannin Isra’ila su taimake ɗansa Solomon.
18 Saying: You see, that the Lord your God is with you, and hath given you rest round about, and hath delivered all your enemies into your hands, and the land is subdued before the Lord, and before his people.
Ya ce musu, “Ba Ubangiji Allahnku yana tare da ku ba? Bai kuma ba ku hutu a kowane gefe ba? Gama ya ba da mazaunan ƙasar gare ni, ƙasar kuma ta Ubangiji ce da mutanensa.
19 Give therefore your hearts and your souls, to seek the Lord your God: and arise, and build a sanctuary to the Lord God, that the ark of the covenant of the Lord, and the vessels consecrated to the Lord, may be brought into the house, which is built to the name of the Lord.
Yanzu fa sai ku sa zuciyarku da ranku ga neman Ubangiji Allahnku. Ku fara ginin wuri mai tsarki na Ubangiji Allah, don ku kawo akwatin alkawarin Ubangiji da kayayyaki masu tsarki na Allah a cikin haikalin da za a gina saboda Sunan Ubangiji.”

< 1 Chronicles 22 >