< 1 Chronicles 14 >

1 And Hiram king of Tyre sent messengers to David, and cedar trees, and masons, and carpenters, to build him a house.
To, fa, Hiram sarkin Taya ya aika da’yan aika zuwa wurin Dawuda, tare da gumaguman al’ul, maginan duwatsu da kafintoci, don su gina wa Dawuda fada.
2 And David perceived that the Lord had confirmed him king over Israel, and that his kingdom was exalted over his people Israel.
Dawuda kuwa ya san cewa Ubangiji ya kafa shi a matsayin sarki a bisa Isra’ila kuma cewa an ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa Isra’ila.
3 And David took other wives in Jerusalem: and he beget sons, and daughters.
A Urushalima, Dawuda ya ƙara auren waɗansu mata, ya kuma zama mahaifin ƙarin’ya’yan maza da mata.
4 Now these are the names of them that were born to him in Jerusalem: Samua, and Sobad, Nathan, and Solomon,
Ga sunayen yaran da aka haifa masa a can. Shammuwa, Shobab, Natan, Solomon,
5 Jebahar, and Elisua, and Eliphalet,
Ibhar, Elishuwa, Elfelet,
6 And Noga, and Napheg, and Japhia,
Noga, Nefeg, Yafiya,
7 Elisama. and Baaliada, and Eliphalet.
Elishama, Beyeliyada da Elifelet.
8 And the Philistines hearing that David was anointed king over all Israel, went all up to seek him: and David heard of it, and went out against them.
Sa’ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda sarki a bisa dukan Isra’ila, sai suka haura da cikakken mayaƙa don su neme shi, amma Dawuda ya ji game da wannan ya kuwa fita don yă ƙara da su.
9 And the Philistines came and spread themselves in the vale of Raphaim.
To, fa, Filistiyawa suka zo suka kai wa Kwarin Refayim hari;
10 And David consulted the Lord, saying: Shall I go up against the Philistines, and wilt thou deliver them into my hand? And the Lord said to him: Go up, and I will deliver them into thy hand.
sai Dawuda ya roƙi Allah ya ce, “In tafi in yaƙi Filistiyawa? Za ka ba da su gare ni?” Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ka tafi, zan ba da su gare ka.”
11 And when they were come to Baalpharasim, David defeated them there, and he said: God hath divided my enemies by my hand, as waters are divided: and therefore the name of that place was called Baalpharasim.
Saboda haka Dawuda da mutanensa suka haura zuwa Ba’al-Ferazim, a can kuwa suka ci Filistiyawa da yaƙi. Sai ya ce, “Kamar yadda ruwa kan raraki ƙasa, haka Allah ya raraki abokan gābana ta wurin hannuna.” Saboda haka aka kira wurin Ba’al-Ferazim.
12 And they left there their gods, and David commanded that they should be burnt.
Filistiyawa suka yashe allolinsu, Dawuda kuma ya ba da umarnai a ƙone su a wuta.
13 Another time also the Philistines made an irruption, and spread themselves abroad in the valley.
Filistiyawa suka sāke kai hari wa kwarin;
14 And David consulted God again, and God said to him: Go not up after them, turn away from them, and come upon them over against the pear trees.
sai Dawuda ya sāke roƙi Allah, Allah kuwa ya amsa masa, “Kada ka tafi kai tsaye, amma ka yi zobe kewaye da su, ka kuma fāɗa musu a gaban itatuwan tsamiya.
15 And when thou shalt hear the sound of one going in the tops of the pear trees, then shalt thou go out to battle. For God is gone out before thee to strike the army of the Philistines.
Da zarar ka ji motsin takawa a sama itatuwan tsamiya, ka fita don yaƙi, domin wannan zai nuna cewa Allah ya fita a gabanka don yă bugi mayaƙan Filistiyawa.”
16 And David did as God had commanded him, and defeated the army of the Philistines, slaying them from Gabaon to Gazera.
Saboda haka Dawuda ya yi kamar yadda Allah ya umarce shi, suka kuma bugi mayaƙan Filistiyawa, tun daga Gibeyon har zuwa Gezer.
17 And the name of David became famous in all countries, and the Lord made all nations fear him.
Sai sunan Dawuda ya bazu ko’ina a ƙasar, Ubangiji kuwa ya sa dukan al’ummai suka ji tsoronsa.

< 1 Chronicles 14 >