< Psalms 95 >
1 Come, let us sing aloud to Jehovah, let us shout for joy to the rock of our salvation;
Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
2 Let us come before his face with thanksgiving; let us shout aloud unto him with psalms.
Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
3 For Jehovah is a great God, and a great king above all gods.
Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
4 In his hand are the deep places of the earth; the heights of the mountains are his also:
A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
5 The sea is his, and he made it, and his hands formed the dry [land].
Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
6 Come, let us worship and bow down; let us kneel before Jehovah our Maker.
Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
7 For he is our God; and we are the people of his pasture and the sheep of his hand. To-day if ye hear his voice,
gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
8 Harden not your heart, as at Meribah, as [in] the day of Massah, in the wilderness;
“Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
9 When your fathers tempted me, proved me, and saw my work.
inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
10 Forty years was I grieved with the generation, and said, It is a people that do err in their heart, and they have not known my ways;
Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
11 So that I swore in mine anger, that they should not enter into my rest.
Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”