< Psalms 83 >
1 A Song; a Psalm of Asaph. O God, keep not silence; hold not thy peace, and be not still, O God:
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 For behold, thine enemies make a tumult; and they that hate thee lift up the head.
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 They take crafty counsel against thy people, and consult against thy hidden ones:
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 They say, Come, and let us cut them off from being a nation, and let the name of Israel be mentioned no more.
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 For they have consulted together with one heart: they have made an alliance together against thee.
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 The tents of Edom and the Ishmaelites, Moab and the Hagarites;
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 Gebal, and Ammon, and Amalek; Philistia, with the inhabitants of Tyre;
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 Asshur also is joined with them: they are an arm to the sons of Lot. (Selah)
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Do unto them as to Midian; as to Sisera, as to Jabin, at the torrent of Kishon:
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 Who were destroyed at Endor; they became as dung for the ground.
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 Make their nobles as Oreb and as Zeeb; and all their chiefs as Zebah and as Zalmunna.
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 For they have said, Let us take to ourselves God's dwelling-places in possession.
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 O my God, make them like a whirling thing, like stubble before the wind.
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 As fire burneth a forest, and as the flame setteth the mountains on fire,
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 So pursue them with thy tempest, and terrify them with thy whirlwind.
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 Fill their faces with shame, that they may seek thy name, O Jehovah.
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 Let them be put to shame and be dismayed for ever, and let them be confounded and perish:
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 That they may know that thou alone, whose name is Jehovah, art the Most High over all the earth.
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.