< Psalms 58 >
1 To the chief Musician. 'Destroy not.' Of David. Michtam. Is righteousness indeed silent? Do ye speak it? Do ye judge with equity, ye sons of men?
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
2 Yea, in heart ye work wickedness; ye weigh out the violence of your hands in the earth.
Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
3 The wicked go astray from the womb; they err as soon as they are born, speaking lies.
Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
4 Their poison is like the poison of a serpent: [they are] like the deaf adder which stoppeth her ear;
Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
5 Which doth not hearken to the voice of enchanters, of one charming ever so wisely.
da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
6 O God, break their teeth in their mouth; break out the great teeth of the young lions, O Jehovah.
Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
7 Let them melt away as waters that flow off; when he aimeth his arrows, let them be as blunted:
Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
8 Let them be as a snail that melteth as it passeth away; [like] the untimely birth of a woman, let them not see the sun.
Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
9 Before your pots feel the thorns, green or burning, — they shall be whirled away.
Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
10 The righteous shall rejoice when he seeth the vengeance; he shall wash his footsteps in the blood of the wicked:
Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
11 And men shall say, Verily there is fruit for the righteous; verily there is a God that judgeth in the earth.
Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”