< Psalms 5 >

1 To the chief Musician. Upon Nehiloth. A Psalm of David. Give ear to my words, O Jehovah; consider my (meditation)
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Busa. Ta Dawuda. Ka saurare kalmomina, ya Ubangiji, ka ji ajiyar zuciyata.
2 Hearken unto the voice of my crying, my king and my God; for to thee will I pray.
Ka saurare kukata na neman taimako, Sarkina da Allahna, gama gare ka nake addu’a.
3 Jehovah, in the morning shalt thou hear my voice; in the morning will I address myself to thee, and will look up.
Da safe, ya Ubangiji, ka ji muryata; da safe na gabatar da bukatuna a gabanka in kuma jira da sa zuciya.
4 For thou art not a God that hath pleasure in wickedness; evil shall not sojourn with thee.
Kai ba Allahn da yake jin daɗin mugu ba ne; gama kana gāba da dukan masu aikata mugunta.
5 Insolent fools shall not stand before thine eyes; thou hatest all workers of iniquity.
Masu fariya ba za su iya tsaya a gabanka ba. Kana ƙin duk masu aikata abin da ba daidai ba.
6 Thou wilt destroy them that speak lies: Jehovah abhorreth a man of blood and deceit.
Kakan hallaka masu yin ƙarya. Masu kisankai da mutane masu ruɗu Ubangiji yana ƙyama.
7 But as for me, in the greatness of thy loving-kindness will I enter thy house; I will bow down toward the temple of thy holiness in thy fear.
Amma ni, ta wurin jinƙanka mai girma, zan shiga gidanka; da bangirma zan durƙusa ga haikalinka.
8 Lead me, Jehovah, in thy righteousness, because of my foes; make thy way plain before me.
Ka bi da ni, ya Ubangiji, cikin adalcinka saboda abokan gābana, ka fayyace hanyarka a gabana.
9 For there is no certainty in their mouth; their inward part is perversion, their throat is an open sepulchre; they flatter with their tongue.
Babu ko kalma guda daga bakinsu da za a dogara da ita; marmarinsu kawai shi ne su hallakar da waɗansu. Maƙogwaronsu buɗaɗɗen kabari ne; da harshensu suna faɗin ƙarya.
10 Bring guilt upon them, O God; let them fall by their own counsels: drive them out in the multitude of their transgressions, for they have rebelled against thee.
Ka furta su masu laifi, ya Allah! Bari makircinsu yă zama fāɗuwarsu. Ka kore su saboda yawan zunubansu, saboda sun tayar maka.
11 And all that trust in thee shall rejoice: for ever shall they shout joyously, and thou wilt protect them; and they that love thy name shall exult in thee.
Amma bari dukan waɗanda suke neman mafaka gare ka su yi murna; bari kullum su yi ta rerawa saboda farin ciki. Ka buɗe kāriyarka a bisansu, domin waɗanda suke ƙaunar sunanka su yi farin ciki a cikinka.
12 For thou, Jehovah, wilt bless the righteous [man]; with favour wilt thou surround him as [with] a shield.
Gama tabbatacce, ya Ubangiji, kakan albarkaci adalai; kakan kewaye su da tagomashinka kamar garkuwa.

< Psalms 5 >