< Psalms 49 >
1 To the chief Musician. Of the sons of Korah. A Psalm. Hear this, all ye peoples; give ear, all inhabitants of the world:
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ku ji wannan, dukanku mutane; ku saurara, dukanku waɗanda suke zama a wannan duniya,
2 Both men of low and men of high degree, rich and poor alike.
babba da yaro mai arziki da talaka.
3 My mouth shall speak wisdom, and the meditation of my heart shall be of understanding:
Bakina zai yi maganar hikima; magana daga zuciyata za tă ba da ganewa.
4 I will incline mine ear to a parable, I will open my riddle upon the harp.
Zan juye kunnena ga karin magana; da garaya zan ƙarfafa kacici-kacicina.
5 Wherefore should I fear in the days of adversity, [when] the iniquity of my supplanters encompasseth me? —
Don me zan ji tsoro sa’ad da mugayen kwanaki suka zo, sa’ad da mugaye masu ruɗu suka kewaye ni,
6 They depend upon their wealth, and boast themselves in the abundance of their riches. ...
waɗanda suka dogara ga arzikinsu suna kuma fariya a kan yawan arzikinsu?
7 None can by any means redeem his brother, nor give to God a ransom for him,
Ba wani da zai iya ceton ran wani ko yă ba wa Allah kuɗin fansa saboda shi,
8 (For the redemption of their soul is costly, and must be given up for ever, )
kuɗin fansa domin rai yana da tsada, babu abin da za a biya da ya taɓa isa,
9 That he should still live perpetually, [and] not see corruption.
da zai sa yă ci gaba da rayuwa har abada yă hana shi shigan kabari yă ruɓa.
10 For he seeth that wise men die; all alike, the fool and the brutish perish, and they leave their wealth to others.
Gama kowa na iya ganin masu hikima na mutuwa; wawaye da marasa azanci su ma kan hallaka su bar wa waɗansu arzikinsu.
11 Their inward thought is, that their houses are for ever, their dwelling-places from generation to generation: they call the lands after their own names.
Kaburburansu za su ci gaba da zama gidajensu har abada, Can za su kasance har zamanai marasa ƙarewa, ko da yake sun ba wa filaye sunayen kansu.
12 Nevertheless, man being in honour abideth not: he is like the beasts that perish.
Amma mutum, kome arzikinsa, ba ya dawwama; shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.
13 This their way is their folly, yet they that come after them delight in their sayings. (Selah)
Wannan ne ƙaddarar waɗanda suke dogara a kansu, da kuma ta mabiyansu, waɗanda suka tabbatar da faɗinsu. (Sela)
14 Like sheep are they laid in Sheol: Death feedeth on them; and the upright shall have dominion over them in the morning; and their comeliness shall be for Sheol to consume, that there be no habitation for them. (Sheol )
Kamar tumaki an ƙaddara su ga kabari; za su kuwa zama abincin mutuwa amma masu gaskiya za su yi mulki a kansu da safe. Kamanninsu za su ruɓe a cikin kabari, nesa da gidajensu masu tsada. (Sheol )
15 But God will redeem my soul from the power of Sheol: for he will receive me. (Selah) (Sheol )
Amma Allah zai ceci raina daga kabari; tabbatacce zai ɗauke ni zuwa wurinsa. (Sela) (Sheol )
16 Be not afraid when a man becometh rich, when the glory of his house is increased:
Kada ka razana da yawa sa’ad da mutum ya yi arziki sa’ad da darajar gidansa ta ƙaru;
17 For when he dieth, he shall carry nothing away; his glory shall not descend after him.
gama ba zai ɗauki kome tare da shi sa’ad da ya mutu ba, darajarsa ba za tă gangara tare da shi ba.
18 Though he blessed his soul in his lifetime, — and men will praise thee when thou doest well to thyself, —
Ko da yake yayinda yake a raye ya ɗauka kansa mai albarka ne, mutane kuma sun yabe ka sa’ad da kake cin nasara,
19 It shall go to the generation of his fathers: they shall never see light.
zai gamu da tsarar kakanninsa, waɗanda ba za su taɓa ganin hasken rayuwa ba.
20 Man that is in honour, and understandeth not, is like the beasts that perish.
Mutumin da yake da arziki ba tare da ganewa ba shi kamar dabbobi ne da suke mutuwa.