< Psalms 147 >
1 Praise ye Jah! for it is good. Sing psalms of our God; for it is pleasant: praise is comely.
Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
2 Jehovah doth build up Jerusalem: he gathereth the outcasts of Israel.
Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
3 He healeth the broken in heart, and bindeth up their wounds.
Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
4 He counteth the number of the stars; he giveth names to them all.
Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
5 Great is our Lord, and of great power: his understanding is infinite.
Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
6 Jehovah lifteth up the meek; he abaseth the wicked to the earth.
Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
7 Sing unto Jehovah with thanksgiving; sing psalms upon the harp unto our God:
Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
8 Who covereth the heavens with clouds, who prepareth rain for the earth, who maketh grass to grow upon the mountains;
Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
9 Who giveth to the cattle their food, to the young ravens which cry.
Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
10 He delighteth not in the strength of the horse, he taketh not pleasure in the legs of a man;
Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
11 Jehovah taketh pleasure in those that fear him, in those that hope in his loving-kindness.
Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
12 Laud Jehovah, O Jerusalem; praise thy God, O Zion.
Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
13 For he hath strengthened the bars of thy gates; he hath blessed thy children within thee;
Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
14 He maketh peace in thy borders; he satisfieth thee with the finest of the wheat.
Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
15 He sendeth forth his oracles to the earth: his word runneth very swiftly.
Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
16 He giveth snow like wool, scattereth the hoar frost like ashes;
Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
17 He casteth forth his ice like morsels: who can stand before his cold?
Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
18 He sendeth his word, and melteth them; he causeth his wind to blow — the waters flow.
Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
19 He sheweth his word unto Jacob, his statutes and his judgments unto Israel.
Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
20 He hath not dealt thus with any nation; and as for [his] judgments, they have not known them. Hallelujah!
Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.