< Psalms 109 >

1 To the chief Musician. Of David. A Psalm. O God of my praise, be not silent:
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Allah, wanda nake yabo, kada ka yi shiru,
2 For the mouth of the wicked [man] and the mouth of deceit are opened against me: they have spoken against me with a lying tongue,
gama mugaye da masu ruɗu sun buɗe bakunansu a kaina; sun yi magana a kaina da harsunan ƙarya.
3 And with words of hatred have they encompassed me; and they fight against me without a cause.
Da kalmomin ƙiyayya sun kewaye ni; sun tasar mini ba dalili.
4 For my love they are mine adversaries; but I [give myself unto] prayer.
A maimakon ƙauna sun sāka mini da zargi, amma ni mutum ne mai addu’a.
5 And they have rewarded me evil for good, and hatred for my love.
Sun sāka mini alheri da mugunta, ƙauna kuma da ƙiyayya.
6 Set a wicked [man] over him, and let [the] adversary stand at his right hand;
Ka naɗa mugun mutum yă yi hamayya da shi; bari mai zargi yă tsaya a hannun damansa.
7 When he shall be judged, let him go out guilty, and let his prayer become sin;
Sa’ad da aka yi masa shari’a, bari a same shi da laifi, bari kuma addu’o’insa su hukunta shi.
8 Let his days be few, let another take his office;
Bari kwanakinsa su zama kaɗan; bari wani yă ɗauki wurinsa na shugabanci.
9 Let his sons be fatherless, and his wife a widow;
Bari’ya’yansa su zama marayu matarsa kuma gwauruwa.
10 Let his sons be vagabonds and beg, and let them seek [their bread] far from their desolate places;
Bari’ya’yansa su zama masu yawo suna bara; bari a yi ta koransu daga gidajensu da suke kufai.
11 Let the usurer cast the net over all that he hath, and let strangers despoil his labour;
Bari mai binsa bashi yă ƙwace dukan abin da yake da shi; bari baƙi su washe amfanin aikinsa.
12 Let there be none to extend kindness unto him, neither let there be any to favour his fatherless children;
Bari kada kowa yă yi masa alheri ko yă ji tausayin marayunsa.
13 Let his posterity be cut off; in the generation following let their name be blotted out:
Bari duk zuriyarsa su mutu, a shafe sunayensu daga tsara mai zuwa.
14 Let the iniquity of his fathers be remembered with Jehovah, and let not the sin of his mother be blotted out;
Bari a tuna da laifin kakanninsa a gaban Ubangiji; bari kada a taɓa shafe zunubin mahaifiyarsa.
15 Let them be before Jehovah continually, that he may cut off the memory of them from the earth:
Bari zunubansu su kasance a gaban Ubangiji kullum, don yă sa a manta da su daga duniya.
16 Because he remembered not to shew kindness, but persecuted the afflicted and needy man, and the broken in heart, to slay him.
Gama bai taɓa yin tunanin yin alheri ba, amma ya tsananta wa matalauta da mabukata da kuma masu fid da zuciya har suka mutu.
17 And he loved cursing; so let it come unto him. And he delighted not in blessing; and let it be far from him.
Yana jin daɗin la’antarwa, bari yă dawo a kansa; ba ya son sa albarka, bari kada kowa yă sa masa albarka.
18 And he clothed himself with cursing like his vestment; so let it come into his bowels like water, and like oil into his bones;
Ya sa la’antarwa kamar rigarsa; ta shiga cikin jikinsa kamar ruwa, cikin ƙasusuwansa kamar mai.
19 Let it be unto him as a garment with which he covereth himself, and for a girdle wherewith he is constantly girded.
Bari tă zama kamar mayafin da aka ɗaura kewaye da shi, kamar ɗamara da aka ɗaura kewaye da shi har abada.
20 Let this be the reward of mine adversaries from Jehovah, and of them that speak evil against my soul.
Bari wannan yă zama sakayyar Ubangiji ga masu zargina, ga waɗanda suke mugayen maganganu a kaina.
21 But do thou for me, Jehovah, Lord, for thy name's sake; because thy loving-kindness is good, deliver me:
Amma kai, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ka yi da ni da kyau saboda sunanka; ta alherin ƙaunarka, ka cece ni.
22 For I am afflicted and needy, and my heart is wounded within me.
Gama ni matalauci ne mai bukata kuma, zuciyata kuwa ta yi rauni a cikina.
23 I am gone like a shadow when it lengtheneth; I am tossed about like the locust;
Na ɓace kamar inuwar yamma; ana kakkaɓe ni kamar fāra.
24 My knees are failing through fasting, and my flesh hath lost its fatness;
Gwiwoyina suna mutuwa saboda azumi; jikina ya rame ba kuma ƙarfi.
25 And I am become a reproach unto them; [when] they look upon me they shake their heads.
Na zama abin dariya ga masu zargina; sa’ad da suka gan ni, suka kaɗa kawunansu.
26 Help me, Jehovah my God; save me according to thy loving-kindness:
Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna; ka cece ni bisa ga ƙaunarka.
27 That they may know that this is thy hand; that thou, Jehovah, hast done it.
Bari su san cewa hannunka ne, cewa kai ne, ya Ubangiji, ka yi shi.
28 Let them curse, but bless thou; when they rise up, let them be ashamed, and let thy servant rejoice.
Za su iya la’anta, amma kai za ka sa albarka; sa’ad da suka tasar za su sha kunya, amma bawanka zai yi farin ciki.
29 Let mine adversaries be clothed with confusion, and let them cover themselves with their shame as with a mantle.
Masu zargina za su sha kunya za a rufe su da kunya kamar mayafi.
30 I will greatly celebrate Jehovah with my mouth; yea, I will praise him among the multitude.
Da bakina zan ɗaukaka Ubangiji sosai; cikin babban taro zan yabe shi.
31 For he standeth at the right hand of the needy, to save him from those that judge his soul.
Gama yana tsaya a hannun damar mai bukata, don yă cece ransa daga waɗanda suke hukunta shi.

< Psalms 109 >