< Proverbs 23 >
1 When thou sittest to eat with a ruler, consider well who is before thee;
Sa’ad da ka zauna domin cin abinci da mai mulki, ka lura sosai da abin da yake gabanka,
2 and put a knife to thy throat, if thou be a man given to appetite.
ka kuma sa wuƙa a maƙogwaronka in kai mai ci da yawa ne.
3 Be not desirous of his dainties; for they are deceitful food.
Kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi gama wannan abinci ruɗu ne.
4 Weary not thyself to become rich; cease from thine own intelligence:
Kada ka gajiyar da kanka don ka yi arziki; ka kasance da hikimar dainawa.
5 wilt thou set thine eyes upon it, it is gone; for indeed it maketh itself wings and it flieth away as an eagle towards the heavens.
Da ƙyiftawar ido a kan wadata ta ɓace, gama tabbatacce sukan yi fikafikai sukan tashi sama kamar gaggafa.
6 Eat thou not the food of him that hath an evil eye, neither desire thou his dainties.
Kada ka ci abincin mai rowa, kada ka yi marmarin abincinsa mai daɗi;
7 For as he thinketh in his soul, so is he. Eat and drink! will he say unto thee; but his heart is not with thee.
gama shi wani irin mutum ne wanda kullum yana tunani game da tsadar abincin. Zai ce maka, “Ci ka sha,” amma zuciyarsa ba ta tare da kai.
8 Thy morsel which thou hast eaten must thou vomit up, and thou wilt have wasted thy sweet words.
Za ka yi amai ɗan abin da ka ci dukan daɗin bakinka kuwa zai tafi a banza.
9 Speak not in the ears of a foolish [man], for he will despise the wisdom of thy words.
Kada ka yi magana da wawa, gama zai yi wa maganar hikimarka ba’a.
10 Remove not the ancient landmark; and enter not into the fields of the fatherless:
Kada ka kawar da shaidar iyaka ta dā ko ka ɗiba gonar marayu,
11 for their redeemer is mighty; he will plead their cause against thee.
gama mai Kāriyarsu yana da ƙarfi; zai kuwa yi magana dominsu.
12 Apply thy heart unto instruction, and thine ears to the words of knowledge.
Ka mai da hankali ga umarni ka kuma kasa kunne ga kalmomin sani.
13 Withhold not correction from the child; for [if] thou beatest him with the rod, he shall not die:
Kada ka bar yaro ba horo; in ka yi masa horo da sanda, ba zai mutu ba.
14 thou shalt beat him with the rod, and shalt deliver his soul from Sheol. (Sheol )
Ka hukunta shi da sanda ka ceci ransa daga mutuwa. (Sheol )
15 My son, if thy heart be wise, my heart shall rejoice, even mine;
Ɗana, in zuciyarka mai hikima ce, to, zuciyata za tă yi murna;
16 and my reins shall exult, when thy lips speak right things.
cikin cikina zai yi farin ciki in leɓunanka suna maganar abin da yake daidai.
17 Let not thy heart envy sinners, but [be thou] in the fear of Jehovah all the day;
Kada ka bar zuciyarka tă yi ƙyashin masu zunubi, amma kullum tsoron Ubangiji za ka yi kishi.
18 for surely there is a result, and thine expectation shall not be cut off.
Tabbatacce akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
19 Thou, my son, hear and be wise, and direct thy heart in the way.
Ka saurara, ɗana, ka zama mai hikima, ka kafa zuciyarka a hanyar da take daidai.
20 Be not among winebibbers, among riotous eaters of flesh.
Kada ka haɗa kai da waɗanda suke shan ruwan inabi da yawa ko masu haɗama kansu da abinci,
21 For the drunkard and the glutton shall come to poverty; and drowsiness clotheth with rags.
gama bugaggu da ruwan inabi da masu yawan ci sukan zama matalauta, gama jiri yakan yi musu sutura da tsummoki.
22 Hearken unto thy father that begat thee, and despise not thy mother when she is old.
Ka kasa kunne ga mahaifinka, wanda ya ba ka rai, kada kuwa ka rena mahaifiyarka sa’ad da ta tsufa.
23 Buy the truth, and sell it not; wisdom, and instruction, and intelligence.
Ka saye gaskiya kada kuwa ka sayar da ita; ka nemi hikima, horo da fahimi.
24 The father of a righteous [man] shall greatly rejoice, and he that begetteth a wise [son] shall have joy of him:
Mahaifin adali yana da farin ciki sosai; duk wanda yake da ɗa mai hikima yakan ji daɗinsa.
25 let thy father and thy mother have joy, and let her that bore thee rejoice.
Bari mahaifinka da mahaifiyarka su yi murna; bari wadda ta haife ka tă yi farin ciki!
26 My son, give me thy heart, and let thine eyes observe my ways.
Ɗana, ka ba ni zuciyarka bari kuma idanunka su kiyaye hanyoyina,
27 For a whore is a deep ditch; and a strange woman is a narrow pit.
gama karuwa rami ne mai zurfi mace marar aminci matsattsiyar rijiya ce.
28 She also lieth in wait as a robber, and increaseth the treacherous among men.
Kamar’yan fashi, takan kwanta tana jira tana kuma ninka rashin aminci a cikin maza.
29 Who hath woe? Who hath sorrow? Who contentions? Who complaining? Who wounds without cause? Who redness of eyes?
Wa yake wayyo? Wa yake baƙin ciki? Wa yake neman fada? Wa yake gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan idanu?
30 — They that tarry long at the wine; they that go to try mixed wine.
Waɗanda suke daɗe suna shan ruwan inabi, waɗanda suke neman ƙoƙon damammen ruwan inabi.
31 Look not upon the wine when it is red, when it sparkleth in the cup, and goeth down smoothly:
Kada ka ƙyifce ido a ruwan inabi sa’ad da ya yi ja, sa’ad da yana da kyan gani a cikin ƙwarya, sa’ad da yana gangarawa sumul a maƙogwaro!
32 at the last it biteth like a serpent, and stingeth like an adder.
A ƙarshe yana sara kamar maciji da kuma dafi kamar gamsheƙa.
33 Thine eyes shall behold strange women, and thy heart shall speak froward things;
Idanunka za su riƙa gane-gane, zuciyarka kuma za su riƙa tunani abubuwa masu rikitarwa.
34 and thou shalt be as he that lieth down in the midst of the sea, and as he that lieth down upon the top of a mast:
Za ka zama kamar wanda yake barci a tsakiyar tekuna, kwance a sama itacen jirgin ruwa.
35 — “They have smitten me, [and] I am not sore; they have beaten me, [and] I knew it not. When shall I awake? I will seek it yet again.”
Za ka ce “Sun buge ni, amma ban ji ciwo ba! Sun daddoke ni, amma ba na jin zafinsa! Yaushe zan farka don in ƙara shan wani?”