< Matthew 10 >
1 And having called to [him] his twelve disciples, he gave them power over unclean spirits, so that they should cast them out, and heal every disease and every bodily weakness.
Sai ya kira almajiransa goma sha biyu wurinsa ya kuma ba su iko su fitar aljanu, su kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya.
2 Now the names of the twelve apostles are these: first, Simon, who was called Peter, and Andrew his brother; James the [son] of Zebedee, and John his brother;
Ga sunayen manzannin nan goma sha biyu, da fari, Siman (wanda ake kira Bitrus) da ɗan’uwansa Andarawus; Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna;
3 Philip and Bartholomew; Thomas, and Matthew the tax-gatherer; James the [son] of Alphaeus, and Lebbaeus, who was surnamed Thaddaeus;
Filibus da Bartolomeyu; Toma da Mattiyu mai karɓar haraji; Yaƙub ɗan Alfayus da Taddayus;
4 Simon the Cananaean, and Judas the Iscariote, who also delivered him up.
Siman Zilot da kuma Yahuda Iskariyot wanda ya bashe Yesu.
5 These twelve Jesus sent out when he had charged them, saying, Go not off into [the] way of [the] nations, and into a city of Samaritans enter ye not;
Waɗannan sha biyun ne Yesu ya aika da umarni cewa, “Kada ku je cikin Al’ummai, ko kuwa ku shiga wani garin Samariyawa.
6 but go rather to the lost sheep of the house of Israel.
A maimakon haka ku je wajen ɓatattun tumakin Isra’ila.
7 And as ye go, preach, saying, The kingdom of the heavens has drawn nigh.
Sa’ad da kuke tafiya, ku yi wa’azi, kuna cewa, ‘Mulkin sama ya kusato.’
8 Heal [the] infirm, [raise the dead], cleanse lepers, cast out demons: ye have received gratuitously, give gratuitously.
Ku warkar da marasa lafiya, ku tā da matattu, ku tsabtacce kutare, ku kuma fitar da aljanu. A kyauta kuka samu, ku kuma bayar a kyauta.
9 Do not provide yourselves with gold, or silver, or brass, for your belts,
“Kada ku riƙe wata zinariya ko azurfa ko jan ƙarfe a aljihunanku,
10 nor scrip for the way, nor two body coats, nor sandals, nor a staff: for the workman is worthy of his nourishment.
kada ku ɗauki jaka don tafiya, ko ƙarin riga, ko takalma ko sanda; domin ma’aikaci ya cancanci hakkinsa.
11 But into whatsoever city or village ye enter, inquire who in it is worthy, and there remain till ye go forth.
Kowane gari ko ƙauyen da kuka shiga, ku nemi mai mutunci a wurin, ku kuma zauna a gidansa har sai kun tashi.
12 And as ye enter into a house salute it.
Da shigarku gidan, ku yi gaisuwa.
13 And if the house indeed be worthy, let your peace come upon it; but if it be not worthy, let your peace return to you.
In gidan na kirki ne, bari salamarku ta zauna a kansa; in kuwa ba mai kirki ba, salamarku ta komo muku.
14 And whosoever shall not receive you, nor hear your words, as ye go forth out of that house or city, shake off the dust of your feet.
Duk wanda ya ƙi marabtarku ko ya ƙi sauraron kalmominku, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku sa’ad da kuka fita gidan ko garin.
15 Verily I say unto you, It shall be more tolerable for the land of Sodom and Gomorrha in judgment-day than for that city.
Gaskiya nake gaya muku, za a fi jin tausayin Sodom da Gomorra a ranar shari’a fiye da wannan gari.
16 Behold, I send you as sheep in the midst of wolves; be therefore prudent as the serpents, and guileless as the doves.
“Ina aikan ku kamar tumaki a cikin kyarketai. Saboda haka ku zama masu wayo kamar macizai, kuma marasa ɓarna kamar kurciyoyi.
17 But beware of men; for they will deliver you up to sanhedrims, and scourge you in their synagogues;
Ku yi hankali da mutane; za su miƙa ku ga majalisa su kuma yi muku bulala a majami’unsu.
18 and ye shall be brought before rulers and kings for my sake, for a testimony to them and to the nations.
Saboda ni, za a ja ku zuwa gaban gwamnoni da gaban sarakuna domin ku ba da shaida a gabansu, da kuma ga Al’ummai.
19 But when they deliver you up, be not careful how or what ye shall speak; for it shall be given to you in that hour what ye shall speak.
Amma sa’ad da suka kama ku, kada ku damu game da abin da za ku faɗa ko kuwa yadda za ku faɗe shi. A lokacin za a ba ku abin da za ku faɗa,
20 For ye are not the speakers, but the Spirit of your Father which speaks in you.
gama ba ku ba ne kuke magana, amma Ruhun Ubanku ne yake magana ta wurinku.
21 But brother shall deliver up brother to death, and father child; and children shall rise up against parents and shall put them to death;
“Ɗan’uwa zai ci amanar ɗan’uwansa, a kuma kashe shi, Uba ma zai yi haka da ɗansa;’ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su.
22 and ye shall be hated of all on account of my name. But he that has endured to [the] end, he shall be saved.
Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya jure har ƙarshe zai sami ceto.
23 But when they persecute you in this city, flee to the other; for verily I say to you, Ye shall not have completed the cities of Israel until the Son of man be come.
Sa’ad da aka tsananta muku a wannan wuri, ku gudu zuwa wancan. Gaskiya nake gaya muku, kafin ku gama zazzaga dukan biranen Isra’ila, Ɗan Mutum zai zo.
24 The disciple is not above his teacher, nor the bondman above his lord.
“Ɗalibi ba ya fin malaminsa, haka ma, bawa ba ya fin maigidansa.
25 [It is] sufficient for the disciple that he should become as his teacher, and the bondman as his lord. If they have called the master of the house Beelzebub, how much more those of his household?
Ya isa wa ɗalibi yă zama kamar malaminsa, haka ma bawa kamar maigidansa. In har an kira wanda yake kan gida Be’elzebub, me za su ce game da mutanen gidansa?
26 Fear them not therefore; for there is nothing covered which shall not be revealed, and secret which shall not be known.
“Saboda haka kada ku ji tsoronsu. Ba abin da yake a rufe da ba za a tone ba, ko kuwa a ɓoye da ba za a bayyana ba.
27 What I say to you in darkness speak in the light, and what ye hear in the ear preach upon the houses.
Abin da na faɗa muku a asirce, ku faɗe shi a sarari; abin da aka faɗa muku a kunne, ku yi shelarsa daga kan rufin ɗaki.
28 And be not afraid of those who kill the body, but cannot kill the soul; but fear rather him who is able to destroy both soul and body in hell. (Geenna )
Kada ku ji tsoron masu kashe jiki amma ba sa iya kashe rai. A maimakon haka, ku ji tsoron Wannan wanda yake da iko yă hallaka rai duk da jiki a jahannama ta wuta. (Geenna )
29 Are not two sparrows sold for a farthing? and one of them shall not fall to the ground without your Father;
Ba akan sayar da kanari biyu kobo ɗaya ba? Duk da haka ba ɗayansu da zai fāɗi ƙasa ba da yardar Ubanku.
30 but of you even the hairs of the head are all numbered.
Kai, ko gashin kanku ma duk an ƙidaya su.
31 Fear not therefore; ye are better than many sparrows.
Saboda haka kada ku ji tsoro; kun fi kanari masu yawa, daraja nesa.
32 Every one therefore who shall confess me before men, I also will confess him before my Father who is in [the] heavens.
“Duk wanda ya bayyana yarda a gare ni a gaban mutane, ni ma zan bayyana yarda a gare shi a gaban Ubana da yake cikin sama.
33 But whosoever shall deny me before men, him will I also deny before my Father who is in [the] heavens.
Amma duk wanda ya yi mūsun sani na a gaban mutane, ni ma zan yi mūsun saninsa a gaban Ubana da yake cikin sama.
34 Do not think that I have come to send peace upon the earth: I have not come to send peace, but a sword.
“Kada fa ku ɗauka na zo ne don in kawo salama a duniya. A’a, ban zo don in kawo salama ba, sai dai takobi.
35 For I have come to set a man at variance with his father, and the daughter with her mother, and the daughter-in-law with her mother-in-law;
Gama na zo ne in sa, “‘gāba tsakanin mutum da mahaifinsa,’ya da mahaifiyarta, matar ɗa da surukarta,
36 and they of his household [shall be] a man's enemies.
abokan gāban mutum, za su zama mutanen gidansa ne.’
37 He who loves father or mother above me is not worthy of me; and he who loves son or daughter above me is not worthy of me.
“Duk wanda ya fi ƙaunar mahaifinsa ko mahaifiyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba; duk kuwa wanda yake ƙaunar ɗansa ko diyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba;
38 And he who does not take up his cross and follow after me is not worthy of me.
duk wanda kuma bai ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, bai dace yă zama nawa ba.
39 He that finds his life shall lose it, and he who has lost his life for my sake shall find it.
Duk mai son adana ransa zai rasa shi, duk wanda kuwa ya rasa ransa saboda ni zai same shi.
40 He that receives you receives me, and he that receives me receives him that sent me.
“Wanda ya karɓe ku, ya karɓe ni ne, wanda kuma ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne.
41 He that receives a prophet in the name of a prophet, shall receive a prophet's reward; and he that receives a righteous man in the name of a righteous man, shall receive a righteous man's reward.
Duk wanda ya karɓi annabi don shi annabi ne, zai sami ladar annabi, duk kuwa wanda ya karɓi mutum mai adalci don shi mai adalci ne, zai sami ladar mai adalci.
42 And whosoever shall give to drink to one of these little ones a cup of cold [water] only, in the name of a disciple, verily I say unto you, he shall in no wise lose his reward.
In kuma wani ya ba wa ɗaya daga cikin ƙananan nan ko da kwaf ruwan sanyi ne kan shi almajirina ne, gaskiya nake gaya muku, ba shakka ba zai rasa ladarsa ba.”