< Mark 7 >
1 And the Pharisees and some of the scribes, coming from Jerusalem, are gathered together to him,
Farisawa suka taru wurin Yesu tare da wadansu marubuta wadda suka zo daga Urushalima.
2 and seeing some of his disciples eat bread with defiled, that is, unwashed, hands,
Sun ga cewa wasu daga cikin almajiransa sun ci gurasa da hannuwa marasa tsabta, wato, basu wanke hannu ba,
3 (for the Pharisees and all the Jews, unless they wash their hands diligently, do not eat, holding what has been delivered by the ancients;
(Domin Farisawa da dukan Yahudawa ba su cin abinci sai dole sun wanke hannu da kyau domin suna kiyaye al'adun dattawa.
4 and [on coming] from the market-place, unless they are washed, they do not eat; and there are many other things which they have received to hold, the washing of cups and vessels, and brazen utensils, and couches),
Idan Farisawa suka dawo daga kasuwa, wajibi ne su yi wanka kamin su ci abinci. Akwai sauran al'adun da suke kiyayewa, kamar wanke moda, tukwane, da wasu santula na dalma, har da dakin cin abinci.)
5 then the Pharisees and the scribes ask him, Why do thy disciples not walk according to what has been delivered by the ancients, but eat the bread with defiled hands?
Farisawa da Marubuta suka tambaye Yesu, “Don me almajiran ka basu kiyaye al'adun dattawa, domin suna cin abinci ba tare da sun wanke hannu ba?”
6 But he answering said to them, Well did Esaias prophesy concerning you hypocrites, as it is written, This people honour me with their lips, but their heart is far away from me.
Amma ya amsa masu cewa, “Ishaya ya yi anabci akan ku masu bautan ganin ido, da ya rubuta cewa 'wadanan mutane suna girmama ni a baka amma zuciyar su tana nesa da ni.
7 But in vain do they worship me, teaching [as their] teachings commandments of men.
Sujadar wofi suke mani suna koyar da ka'idodi na mutane a matsayin rukunansu'”.
8 [For], leaving the commandment of God, ye hold what is delivered by men [to keep] — washings of vessels and cups, and many other such like things ye do.
Kun watsar da dokar Allah sai kuka rungumi al'adun mutane.
9 And he said to them, Well do ye set aside the commandment of God, that ye may observe what is delivered by yourselves [to keep].
Sai yace masu, kun yi nasara wurin kau da dokokin Allah domin ku kiyaye al'adun ku na mutane.
10 For Moses said, Honour thy father and thy mother; and, he who speaks ill of father or mother, let him surely die.
Koda shike Musa ya rubuta cewa, “ka girmama Ubanka da Uwarka”, kuma, “duk wanda ya zagi Ubansa ko Uwatasa, ya cancanci mutuwa nan take”.
11 But ye say, If a man say to his father or his mother, [It is] corban (that is, gift), whatsoever thou mightest have profit from me by...
Amma kun ce, 'idan mutum ya ce wa iyayensa, “duk taimakon da ya cacanci ku samu daga guna ya zama kebabbe (wato, 'na mika wa Allah)”'.
12 And ye no longer suffer him to do anything for his father or his mother;
Sabo da haka, kun ba shi izini kada ya yi wa Ubansa ko Uwatasa wani abu.
13 making void the word of God by your traditional teaching which ye have delivered; and many such like things ye do.
Kuna mayar da dokan Allah abin banza, sabili da al'adun ku da kuka mika masu. Wannan, da wasu abubuwa kamar haka kuke yi.”
14 And having called again the crowd, he said to them, Hear me, all [of you], and understand:
Ya kara kiran taron jama'ar yace masu, “ku kasa kunne gareni, kuma ku gane.
15 There is nothing from outside a man entering into him which can defile him; but the things which go out from him, those it is which defile the man.
Babu wani abu daga wajen mutum da zai iya gurbatar da shi har idan ya shiga cikinsa. Amma, abinda ya fita daga cikinsa shike gurbatar da shi”
16 If any one have ears to hear, let him hear.
Bari mai kunnen ji, ya ji.
17 And when he went indoors from the crowd, his disciples asked him concerning the parable.
Da Yesu ya bar taron jama'ar, ya shiga gida, sai almajiransa suka tambaye shi ma'anar wannan misali.
18 And he says to them, Are ye also thus unintelligent? Do ye not perceive that all that is outside entering into the man cannot defile him,
Sai Yesu yace, 'ashe baku da ganewa? ko baku sani cewa abin da ya shiga cikin mutum daga waje ba zai iya gurbatar da shi ba,
19 because it does not enter into his heart but into his belly, and goes out into the draught, purging all meats?
domin ba zai iya kai wa cikin zuciyarsa ba, sai dai ya shiga cikin sa ya kuma fita a matsayin bayan gari a salga”. Da wannan magana, Yesu ya mayar da dukan abinci ya zama da tsabta.
20 And he said, That which goes forth out of the man, that defiles the man.
Ya ce, abinda ke cikin mutum shike gurbatar da shi
21 For from within, out of the heart of men, go forth evil thoughts, adulteries, fornications, murders,
Domin daga cikin mutum, kuma daga cikin zuciyarsa ne, mugun tunani, lalata, sata, kisa,
22 thefts, covetousness, wickednesses, deceit, licentiousness, a wicked eye, injurious language, haughtiness, folly;
zina, kwadayi, mugunta, hai'inci, mugun guri, kishi, zargi, girmankai, wawanci.
23 all these wicked things go forth from within and defile the man.
Duk wadannan miyagun abubuwa suna fitowa ne daga cikin mutum, kuma suke gurbatar da shi.”
24 And he rose up and went away thence into the borders of Tyre and Sidon; and having entered into a house he would not have any one know [it], and he could not be hid.
Ya tashi daga nan ya tafi shiyyar Sur da Sida. Ya shiga wani gida don baya son wani ya sani cewa yana nan, amma bai iya boyuwa ba.
25 But immediately a woman, whose little daughter had an unclean spirit, having heard of him, came and fell at his feet
Amma nan da nan wata mace, wadda diyarta ke da mugun ruhu-wannan mace kuwa ta ji game da Yesu sai ta zo ta durkusa a gabansa.
26 (and the woman was a Greek, Syrophenician by race), and asked him that he would cast the demon out of her daughter.
Matar yar kasar Girka ce, kuma asalinta daga Fonishiya take. Ta roke shi da ya fitar da mugun ruhun nan daga diyarta.
27 But [Jesus] said to her, Suffer the children to be first filled; for it is not right to take the children's bread and cast it to the dogs.
Sai ya ce mata, “Bari a ciyar da 'ya'ya tukuna. Domin bai kamata a dauki abincin yaya a ba karnuka ba”.
28 But she answered and says to him, Yea, Lord; for even the dogs under the table eat of the children's crumbs.
Sai ta amsa masa cewa, “I, Ubangiji, Karnukan ma sukan ci abincin da ke fadowa daga teburin 'ya'yan.”
29 And he said to her, Because of this word, go thy way, the demon is gone out of thy daughter.
Ya ce mata, “domin kin fadi haka, kina iya ki tafi domin aljani ya fita daga diyarki.”
30 And having gone away to her house she found the demon gone out, and her daughter lying on the bed.
Ta koma gida sai ta iske diyarta na kwance akan gado, aljanin ya fice daga jikinta.
31 And again having left the borders of Tyre and Sidon, he came to the sea of Galilee, through the midst of the coasts of Decapolis.
Ya sake fita daga shiyar Sur, ya biyo ta Sidon, har zuwa tekun Galili a shiyar Dikafolis.
32 And they bring to him a deaf [man] who could not speak right, and they beseech him that he might lay his hand on him.
Sun kawo masa wani kurma, kuma bebe ne shi, suna rokansa ya dora hanuwansa a bisansa.
33 And having taken him away from the crowd apart, he put his fingers to his ears; and having spit, he touched his tongue;
Sai ya jawo shi daga taron jama'ar, zuwa gefe, sai ya sa hanunsa a kunuwan beben bayan ya tufa yawunsa, sannan ya taba harshensa.
34 and looking up to heaven he groaned, and says to him, Ephphatha, that is, Be opened.
Ya dubi sama, ya ja numfashi ya ce masa, “Ifatha”, wato, “bude!”
35 And immediately his ears were opened, and the band of his tongue was loosed and he spoke right.
Nan da nan ya mayar masa da jinsa. abinda ya daure harshensa ya sake shi, sai ya fara magana da kyau.
36 And he charged them that they should speak to no one [of it]. But so much the more he charged them, so much the more abundantly they proclaimed it;
Ya umarce su da kada su gaya wa wani. Amma duk da umarnin da yake basu, suna ta shaida shi ko'ina.
37 and they were astonished above measure, saying, He does all things well; he makes both the deaf to hear, and the speechless to speak.
kuma suna ta mamaki cewa, “Yayi kowanne abu da kyau, har ya sa kurame suna jin magana, da kuma bebaye na magana.”