< Mark 3 >

1 And he entered again into the synagogue; and there was there a man having his hand dried up.
Sai kuma ya sake tafiya cikin Majami'a sai ga wani Mutum mai shanyayyen hannu.
2 And they watched him if he would heal him on the sabbath, that they might accuse him.
Wadansu mutane suna kallonsa sosai, su gani ko zai warkar da shi a ranar Asabar. don su zarge shi.
3 And he says to the man who had his hand dried up, Rise up [and come] into the midst.
Yesu ya ce wa mai shanyayyen hanun “Ka tashi ka tsaya a tsakiyar kowa.”
4 And he says to them, Is it lawful on the sabbath to do good or to do evil, to save life or to kill? But they were silent.
Sai ya ce wa mutane, “Ya dace a yi abu mai kyau aranar Asabar ko a yi mugunta; a ceci rai, ko a yi kisa? “Amma suka yi shiru.
5 And looking round upon them with anger, distressed at the hardening of their heart, he says to the man, Stretch out thy hand. And he stretched [it] out, and his hand was restored.
Sai ya dube su cikin fushi, yana bakin ciki da taurin zuciyar su, ya ce wa mutumin ka mikar da hanunka, sai ya mikar da hanunsa Yesu kuwa ya warkar da shi.
6 And the Pharisees going out straightway with the Herodians took counsel against him, how they might destroy him.
Sai Farisiyawa suka fita da sauri zuwa wurin mutanen Hirudus suka shirya yadda za su kashe shi.
7 And Jesus withdrew with his disciples to the sea; and a great multitude from Galilee followed him, and from Judaea,
Sai Yesu da almajiransa, suka tafi bakin teku. sai mutane dayawa suka bi shi, daga Galili da Yahudiya
8 and from Jerusalem, and from Idumaea and beyond the Jordan; and they of around Tyre and Sidon, a great multitude, having heard what things he did, came to him.
Daga Urushalima da Edom gaba da Urdun da kewayan Taya da Sidon, da baban taro, ya ji abinda yake yi. suka zo wurinsa.
9 And he spoke to his disciples, in order that a little ship should wait upon him on account of the crowd, that they might not press upon him.
Ya tambayi almajiransa su shirya masa karamin jirgin ruwa domin yawan mutane, domin kada su murkushe shi.
10 For he healed many, so that they beset him that they might touch him, as many as had plagues.
Ya warkar da mutane da yawa, yadda duk wadanda suke da cuttutuka suna kokari su taba shi.
11 And the unclean spirits, when they beheld him, fell down before him, and cried saying, Thou art the Son of God.
Duk sa'adda kazaman ruhohin suka ganshi, sai su durkusa a gabansa su yi ihu da karfi su ce, kai Dan Allah ne.”
12 And he rebuked them much, that they might not make him manifest.
Ya umarce su da karfi kada su sa a san shi.
13 And he goes up into the mountain, and calls whom he himself would, and they went to him.
Ya hau saman dutsen, ya kira wadanda yake bukar su, su zo wurinsa.
14 And he appointed twelve that they might be with him, and that he might send them to preach,
Ya zabi guda goma sha biyu (ya kira su manzanni). Wadanda zasu kasance tare da shi, ya kuma aike su, su yi wa, azi,
15 and to have power [to heal diseases, and] to cast out demons.
Ya kuma basu Ikon fitar da aljanu.
16 And he gave to Simon the surname of Peter;
Ya zabi guda goma sha biyu wato Saminu kuma yaba shi suna Bitrus.
17 and James the [son] of Zebedee, and John the brother of James, and he gave them the surname of Boanerges, that is, Sons of thunder;
Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan-uwan Yakubu wanda ya basu sunan Buwanarjis watau 'ya'yan tsawa,
18 and Andrew, and Philip, and Bartholomew, and Matthew, and Thomas, and James the [son] of Alphaeus, and Thaddaeus, and Simon the Cananaean,
da Andarawus da Filibus da Bartalamawus da Matta da Toma da Yakubu dan Halfa, da Taddawus da Saminu Ba-kananiye,
19 and Judas Iscariote, who also delivered him up. And they come to [the] house.
da Yahuza Iskariyoti wanda zai bashe shi.
20 And again a crowd comes together, so that they cannot even eat bread.
Sa'adda ya shiga gida, Taron kuwa ya sake haduwa, har ya hana su cin abinci,
21 And his relatives having heard [of it] went out to lay hold on him, for they said, He is out of his mind.
Da iyalansa suka ji haka, sai suka fito sun kamo shi, saboda sun ce, “Ai, baya cikin hankalinsa “
22 And the scribes who had come down from Jerusalem said, He has Beelzebub, and, By the prince of the demons he casts out demons.
Marubutan da suka zo daga Urushalima suka ce “Ai Ba'alzabuba ne ya hau shi, da ikon sarkin aljannu kuma yake fitar da aljannu.”
23 And having called them to [him], he said to them in parables, How can Satan cast out Satan?
Yesu ya kirawo su wurinsa ya ce da su cikin misalai, “Yaya shaidan zai iya fitar da shaidan?
24 And if a kingdom has become divided against itself, that kingdom cannot subsist.
idan mulki ya rabu gida biyu ba zai tsayawa ba.
25 And if a house has become divided against itself, that house cannot subsist.
Haka in gida ya rabu kashi biyu, gaba da kansa bai zai tsaya ba.
26 And if Satan rise up against himself, and is divided, he cannot subsist, but has an end.
Shaidan kuma in ya tayar wa kansa ya rabu, ba zai iya tsayawa ba, gama karshen sa ya zo kenan.
27 But no one can, having entered into his house, plunder the goods of the strong [man] unless he first bind the strong [man], and then he will plunder his house.
Amma ba mai iya shiga gidan kakkarfan mutum ya kwace kayansa, ba tare da ya fara daure kakkarfan mutumin ba, sa'an nan kuma ya kwashe kayan gidansa.
28 Verily I say unto you, that all sins shall be forgiven to the sons of men, and all the injurious speeches [with] which they may speak injuriously;
Hakika, ina gaya maku, dukan zunuban da mutane suka yi za a gafarta masu, da kowane irin sabon da suka furta,
29 but whosoever shall speak injuriously against the Holy Spirit, to eternity has no forgiveness; but lies under the guilt of an everlasting sin; (aiōn g165, aiōnios g166)
amma fa duk wanda yayi sabon Ruhun Mai Tsarki baza a gafarta masa ba ko kadan, ya zama mai zunubi har abada.” (aiōn g165, aiōnios g166)
30 — because they said, He has an unclean spirit.
“Yesu ya fadi wadannan abubuwa domin suna cewa yana da ba kazamin ruhu,”
31 And his brethren and his mother come, and standing without sent to him calling him.
Sa'an nan uwatasa, da “Yan'uwansa suka zo suna tsaye a waje. sai suka aika masa, suna kuma umurtar sa ya zo.
32 And a crowd sat around him. And they said to him, Behold, thy mother and thy brethren seek thee without.
Taro kuwa na zaune kewaye da shi, sai suka yi magana da shi da cewa, ga uwarka da yan-uwanka suna nan a waje, suna nemanka.”
33 And he answered them, saying, Who is my mother or my brethren?
Ya amsa masu, “Dacewa su wanene uwa-ta da “yan'uwa na? “
34 And looking around in a circuit at those that were sitting around him, he says, Behold my mother and my brethren:
Sai ya waiwayi wadanda suke zaune kewaye da shi, yace, “Ga uwa-ta da yan-uwana anan!
35 for whosoever shall do the will of God, he is my brother, and sister, and mother.
Gama duk wanda ke yin abin da Allah yake so, shine dan'uwana da yar, uwata, da kuma uwa-ta.”

< Mark 3 >