< Mark 12 >

1 And he began to say to them in parables, A man planted a vineyard, and made a fence round [it] and dug a wine-vat, and built a tower, and let it out to husbandmen, and left the country.
Sai Yesu ya fara koyar da su da misalai. “Wani mutum ne ya yi gonar inabi ya shingen ta, ya haka ramin matse inabin, ya kuwa gina hasumayar tsaro. Ya ba wandansu manoma jinginar gonar, sa'an nan ya tafi wata kasa mai nisa.
2 And he sent a bondman to the husbandmen at the season, that he might receive from the husbandmen of the fruit of the vineyard.
Da lokaci ya yi, sai ya aika masu wani bawansa domin ya karbi wadansu daga cikin amfanin gonar.
3 But they took him, and beat [him], and sent [him] away empty.
Amma manoman suka kama shi, suka yin masa duka, suka kore shi hannu banza.
4 And again he sent to them another bondman; and [at] him they [threw stones, and] struck [him] on the head, and sent [him] away with insult.
Ya sake aikar wani bawan. Shi kuma suka raunata shi aka, suka wulakanta shi.
5 And [again] he sent another, and him they killed; and many others, beating some and killing some.
Ya sake aiken wani. Shi kam, suka kashe shi. Haka fa aka yi ta yi da wadansu da yawa, sun dodoki wadansu, suka kuma kashe wadansu.
6 Having yet therefore one beloved son, he sent also him to them the last, saying, They will have respect for my son.
Yanzu dai yana da sauran daya tak, shine kaunatacen dansa. Daga karshe ya aike shi wurinsu, yana cewa, ai za su bashi girma.
7 But those husbandmen said to one another, This is the heir: come, let us kill him and the inheritance will be ours.
Amma manoman nan suka ce wa juna, “ai, wannan shine magajinsa, 'ku zo mu kashe shi, gadon ya zama namu.”
8 And they took him and killed him, and cast him forth out of the vineyard.
Sai suka kamo shi, suka kashe shi, suka jefar da shi bayan shinge.
9 What therefore shall the lord of the vineyard do? He will come and destroy the husbandmen, and will give the vineyard to others.
To, me mai gonar inabin zai yi? Sai ya zo ya hallaka manoman nan, ya ba wadansu gonar.
10 Have ye not even read this scripture, The stone which they that builded rejected, this has become the corner-stone:
Ashe, ba ku karanta wannan nassi ba? cewa, ' Dutsen da magina suka ki, shi ne ya zama mafi mahmimanci.
11 this is of [the] Lord, and it is wonderful in our eyes?
Wannan daga Ubangiji ne, kuma ya yi dai dai a idanunmu.”'
12 And they sought to lay hold of him, and they feared the crowd; for they knew that he had spoken the parable of them. And they left him and went away.
Sai suka nemi su kama shi, don sun lura a kansu ne ya yi masalin, amma suka ji tsoron jama'a. Don haka suka kyele shi, suka tafi.
13 And they send to him certain of the Pharisees and of the Herodians, that they might catch him in speaking.
Suka aika masa da wadansu farisiyawa da Heridiyawa, don su sa masa tarko da kalamai cikin maganarsa.
14 And they come and say to him, Teacher, we know that thou art true, and carest not for any one; for thou regardest not men's person, but teachest the way of God with truth: Is it lawful to give tribute to Caesar or not?
Da suka zo, suka ce masa, “Malam, gaskiya kana koyar da maganar Allah sosai, ba ka nuna bambanci tsakani mutane, sai koyar da tafarkin Allah kake yi sosai. “Shin, mu biya haraji ga Kaisar, ko a a?”
15 Should we give, or should we not give? But he knowing their hypocrisy said unto them, Why tempt ye me? Bring me a denarius that I may see [it].
AmmaYesu ya gane munafuncinsu, ya ce masu, “Don me kuke gwada ni? ku kawo mani dinarin in gani.”
16 And they brought [it]. And he says to them, Whose [is] this image and superscription? And they said to him, Caesar's.
Suka kawowa Yesu daya. Ya ce masu, “Kamar waye da kuma rubutun wanene? suka ce masa, “Na Kaisar ne.”
17 And Jesus answering said to them, Pay what is Caesar's to Caesar, and what is God's to God. And they wondered at him.
Yesu ya ce, “to, ku ba Kaisar abinda yake na Kaisar, ku kuma ba Allah abin da yake na Allah. Sai suka yi mamakinsa kwarai.
18 And Sadducees come to him, that say there is no resurrection; and they demanded of him saying,
Sai Sadukiyawa suka zo wurinsa, su dake cewa babu tashin matattu. Suka tambaya shi suka ce,
19 Teacher, Moses wrote to us that if any one's brother die, and leave a wife behind, and leave no children, that his brother shall take his wife, and raise up seed to his brother.
“Malam, Musa dai ya rubuta mana, cewa idan dan'uwan mutum ya mutu, ya bar matarsa ba da, lallai ne dan'uwan mutumin ya auri matar, ya haifa wa dan'uwansa 'ya'ya.'
20 There were seven brethren; and the first took a wife, and dying did not leave seed;
To an yi wadansu 'yan'uwa maza guda bakwai, na farko ya yi aure, ya mutu bai bar 'ya'ya ba.
21 and the second took her and died, and neither did he leave seed; and the third likewise.
Na biyu kuma ya aure ta, shi ma ya mutu, ba 'ya'ya. Na ukun ma haka.
22 And the seven [took her and] did not leave seed. Last of all the woman also died.
Haka dai duk bakwai din, ba wanda ya bar 'ya'ya. A karshe kuma ita matar ta mutu.
23 In the resurrection, when they shall rise again, of which of them shall she be wife, for the seven had her as wife?
To, a tashin matattu, matar wa za ta zama a cikinsu? Don duk bakwai din nan sun aure ta”.
24 And Jesus answering said to them, Do not ye therefore err, not knowing the scriptures, nor the power of God?
Sai Yesu ya ce, “Ba saboda wannan dalili ne kuka yi kuskure ba, wato don ba ku san littafin ba, kuma ba ku san ikon Allah ba?
25 For when they rise from among [the] dead they neither marry, nor are given in marriage, but are as angels [who are] in the heavens.
Domin in an tashin daga matattu, ba a aure, ba a auraswa, amma sun zama kamar malaiku a sama.
26 But concerning the dead that they rise, have ye not read in the book of Moses, in [the section of] the bush, how God spoke to him, saying, I [am] the God of Abraham, and the God of Isaac, and the God of Jacob?
Amma game da mattattun da suka tashi, ashe, ba ku taba karantawa a littafin Musa ba, yadda Allah ya ce masa? “Ni ne Allah na Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu'?
27 He is not the God of [the] dead, but of [the] living. Ye therefore greatly err.
Ai, shi ba Allahn mattatu bane, amma na rayyayu ne. Hakika kun yi kuskure “.
28 And one of the scribes who had come up, and had heard them reasoning together, perceiving that he had answered them well, demanded of him, Which is [the] first commandment of all?
Sai wani malamin attuara ya zo ya ji suna muhawara da juna. Da dai ya ga Yesu yana ba su kyakkyawar amsa, sai ya tambaye shi, “Wanne Umarni ne mafi girma dukka?”
29 And Jesus answered him, [The] first commandment of all [is], Hear, Israel: the Lord our God is one Lord;
Yesu ya amsa yace, “mafi girma shine, 'ku saurara ya Isra'ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji daya ne.
30 and thou shalt love the Lord thy God with all thy heart, and with all thy soul, and with all thine understanding, and with all thy strength. This is [the] first commandment.
Sai ka kaunaci Ubangiji Allah da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka da dukkan tunaninka, da dukkan karfinka.
31 And a second like it [is] this: Thou shalt love thy neighbour as thyself. There is not another commandment greater than these.
ta biyu itace, 'ka kaunaci makwabcinka kamar kanka, Ba wata doka da ta fi wadannan.''
32 And the scribe said to him, Right, teacher; thou hast spoken according to [the] truth. For he is one, and there is none other besides him;
Sai malamin attaura ya ce masa, “Hakika gaskiyarka malam, Allah daya ne, ba kuma wani sai shi.
33 and to love him with all the heart, and with all the intelligence, and with all the soul, and with all the strength, and to love one's neighbour as one's self, is more than all the burnt-offerings and sacrifices.
A kaunace shi kuma da dukkan zuciya, da dukkan hankali, da dukkan karfi, a kuma kaunaci makwabci kamar kanka, ai ya fi dukkan hadayu na konawa.”
34 And Jesus, seeing that he had answered intelligently, said to him, Thou art not far from the kingdom of God. And no one dared question him any more.
Da Yesu ya ga ya yi masa magana da hikima, sai ya ce masa, “Ba ka nesa da mulkin Allah.” Bayan wannan kuma ba wanda ya sake tambayarsa wani abu.
35 And Jesus answering said [as he was] teaching in the temple, How do the scribes say that the Christ is son of David?
Yesu ya amsa a lokacin da yake koyarwa a Haikali, ya ce “Yaya malaman attaura suke ce wa Kristi dan Dauda ne?
36 [for] David himself said [speaking] in the Holy Spirit, The Lord said to my Lord, Sit on my right hand until I put thine enemies [as] footstool of thy feet.
Domin Dauda kansa, ta ikon Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Ubangiji ya ce wa Ubangijina, zauna a hannun damana, har sai na kaskantar da makiyanka'.
37 David himself [therefore] calls him Lord, and whence is he his son? And the mass of the people heard him gladly.
Dauda da kansa ya kira shi 'Ubangiji; To, ta yaya ya Almasihu zai zama Dan Dauda?” Babban taron jama'ar suka saurare shi da murna.
38 And he said to them in his doctrine, Beware of the scribes, who like to walk about in long robes, and salutations in the marketplaces,
A koyarwa sa Yasu ya ce, “ku yi hankali da malaman attaura, masu son yawo da manyan riguna, suna so a gaishesu a kasuwa,
39 and first seats in the synagogues, and first places at suppers;
da kuma son wuraren zama masu daraja a haikali, da wurin bukukuwa.
40 who devour the houses of widows, and as a pretext make long prayers. These shall receive a severer judgment.
Sun kuma kwace gidajen gwauraye, da yin doguwar addu'a, don mutane su gani. Wadanan mutanen zasu sami hukunci mai tsanani.”
41 And Jesus, having sat down opposite the treasury, saw how the crowd was casting money into the treasury; and many rich cast in much.
Sai ya zauna a gaban akwatin baiko a Haikalin, yana duban yadda jama'a suke zuba kudi a ciki.
42 And a poor widow came and cast in two mites, which is a farthing.
Wadansu masu arziki da yawa suna zuba kudi masu tsoka. Sai gwauruwa mara abin hanu ta saka anini biyu a ciki akwatin baikon.
43 And having called his disciples to [him] he said to them, Verily I say unto you, This poor widow has cast in more than all who have cast into the treasury:
Ya kira almajiransa, ya ce masu, “Hakika, ina gaya maku, abinda gwauruwa nan ta saka a akwatin baikon nan ya fi na sauran dukka.
44 for all have cast in of that which they had in abundance, but she of her destitution has cast in all that she had, the whole of her living.
Su duk sun bayar daga yalwa tasu ne, ita kuwa daga cikin rashinta ta bada duk abinda take da shi.”

< Mark 12 >