< Luke 20 >
1 And it came to pass on one of the days, as he was teaching the people in the temple, and announcing the glad tidings, the chief priests and the scribes with the elders came up,
Wata rana da Yesu yana koyar da mutane, yana musu wa’azin bishara a filin haikalin, sai manyan firistoci da malaman dokoki, tare da dattawan suka zo wurinsa.
2 and spoke to him saying, Tell us by what authority thou doest these things, or who is it who has given thee this authority?
Suka ce masa, “Gaya mana, da wane iko kake yin waɗannan abubuwa. Wa ya ba ka wannan ikon?”
3 And he answering said to them, I also will ask you [one] thing, and tell me:
Ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku faɗa mini,
4 The baptism of John, was it of heaven or of men?
baftismar Yohanna, daga sama ne ta fito, ko kuwa daga wurin mutane ne?”
5 And they reasoned among themselves, saying, If we should say, Of heaven, he will say, Why have ye not believed him?
Sai suka yi shawara da junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai tambaya, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
6 but if we should say, Of men, the whole people will stone us, for they are persuaded that John was a prophet.
Amma in kuma muka ce, ‘Daga mutane ne,’ dukan mutanen za su jajjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata cewa, Yohanna annabi ne.”
7 And they answered, they did not know whence.
Don haka, sai suka amsa cewa, “Ba mu san inda ta fito ba.”
8 And Jesus said to them, Neither do I tell you by what authority I do these things.
Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku, ko da wane iko ne, nake yin waɗannan abubuwa ba.”
9 And he began to speak to the people this parable: A man planted a vineyard and let it out to husbandmen, and left the country for a long time.
Sai ya ci gaba da gaya wa mutanen wannan misali ya ce, “Wani mutum ya yi gonar inabi, sai ya ba da hayarta ga waɗansu manoma, sa’an nan ya yi wata doguwar tafiya.
10 And in the season he sent to the husbandmen a bondman, that they might give to him of the fruit of the vineyard; but the husbandmen, having beaten him, sent [him] away empty.
A lokacin girbi, sai ya aiki bawa zuwa wurin masu hayan, don su ba shi daga cikin’ya’yan inabin. Amma’yan hayan suka yi wa bawan nan dūka, suka kore shi hannu wofi.
11 And again he sent another bondman; but they, having beaten him also, and cast insult upon him, sent [him] away empty.
Ya sāke aikan wani bawa, shi ma suka yi masa dūka, suka kunyata shi, suka kuma kore shi hannu wofi.
12 And again he sent a third; and they, having wounded him also, cast [him] out.
Har yanzu, ya sāke aikan na uku, amma suka ji masa rauni, suka jefar da shi waje.
13 And the lord of the vineyard said, What shall I do? I will send my beloved son: perhaps when they see him they will respect [him].
“Sai mai gonar inabin ya ce, ‘Me zan yi? Zan aiki ɗana da nake ƙauna, wataƙila za su girmama shi.’
14 But when the husbandmen saw him, they reasoned among themselves, saying, This is the heir; [come, ] let us kill him, that the inheritance may become ours.
“Amma da’yan hayan suka gan shi, sai suka tattauna zancen, suka ce, ‘Wannan shi ne magājin, mu kashe shi sa’an nan gādon zai zama namu!’
15 And having cast him forth out of the vineyard, they killed [him]. What therefore shall the lord of the vineyard do to them?
Sai suka fitar da shi waje, suka kashe shi. “To, me mai gonar inabin zai yi da su?
16 He will come and destroy those husbandmen, and will give the vineyard to others. And when they heard it they said, May it never be!
Zai zo ya karkashe masu hayan nan, ya ba wa waɗansu gonar inabin.” Da mutanen suka ji wannan, sai suka ce, “Allah ya sawwaƙa!”
17 But he looking at them said, What then is this that is written, The stone which they that builded rejected, this has become the corner-stone?
Yesu ya zura musu ido ya ce, “To, mene ne ma’anar abin da aka rubuta cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kan ginin’
18 Every one falling on this stone shall be broken, but on whomsoever it shall fall, it shall grind him to powder.
Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Kuma in dutsen nan ya fāɗi a kan wani, zai murƙushe shi.”
19 And the chief priests and the scribes sought the same hour to lay hands on him, and they feared the people; for they knew that he had spoken this parable of them.
Malaman dokoki da manyan firistoci, suka nemi hanyar kama shi nan da nan, domin sun san cewa, ya yi wannan misali a kansu ne, amma suna jin tsoron mutane.
20 And having watched [him], they sent out suborned persons, pretending to be just men, that they might take hold of him in [his] language, so that they might deliver him up to the power and authority of the governor.
Sai suka sa masa ido, suka aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka nuna kamar su masu gaskiya ne, suna nufin su kama shi game da abin da zai faɗa, domin su ba da shi ga gwamna mai mulki, da mai iko.
21 And they asked him saying, Teacher, we know that thou sayest and teachest rightly, and acceptest no [man's] person, but teachest with truth the way of God:
Sai’yan leƙen asirin suka tambaye shi, suka ce, “Malam, mun sani kana faɗin, kuma kana koyar da abin da yake daidai, ba ka kuma nuna bambanci, amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya.
22 Is it lawful for us to give tribute to Caesar, or not?
Daidai ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
23 But perceiving their deceit he said to them, Why do ye tempt me?
Ya gane makircinsu, sai ya ce musu,
24 Shew me a denarius. Whose image and superscription has it? And answering they said, Caesar's.
“Nuna mini dinari. Hoton wane ne, kuma rubutun wane ne a kai?” Suka amsa, “Na Kaisar.”
25 And he said to them, Pay therefore what is Caesar's to Caesar, and what is God's to God.
Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”
26 And they were not able to take hold of him in [his] expressions before the people, and, wondering at his answer, they were silent.
Ba su iya kama shi a kan abin da ya faɗa a fili ba. Amsarsa ya ba su mamaki, shi ya sa suka yi shiru.
27 And some of the Sadducees, who deny that there is any resurrection, coming up [to him],
Waɗansu Sadukiyawa da suke cewa, ba tashin matattu, suka zo wurin Yesu da tambaya cewa,
28 demanded of him saying, Teacher, Moses wrote to us, If any one's brother, who has a wife, die, and he die childless, his brother shall take the wife and raise up seed to his brother.
“Malam, Musa ya rubuta mana cewa, ‘In ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata amma ba’ya’ya, dole mutumin ya aure gwauruwar, ya samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.’
29 There were then seven brethren: and the first, having taken a wife, died childless;
To, an yi waɗansu’yan’uwa bakwai. Na fari ya auri wata mace, ya mutu ba’ya’ya.
30 and the second [took the woman, and he died childless];
Na biyun,
31 and the third took her: and in like manner also the seven left no children and died;
da na ukun suka aure ta. Haka nan dukansu bakwai suka mutu babu’ya’ya.
32 and last of all the woman also died.
A ƙarshe, ita macen ma ta mutu.
33 In the resurrection therefore of which of them does she become wife, for the seven had her as wife?
Shin, a tashin matattu, matar wa za tă zama? Tun da su bakwan nan, sun aure ta.”
34 And Jesus said to them, The sons of this world marry and are given in marriage, (aiōn )
Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure, (aiōn )
35 but they who are counted worthy to have part in that world, and the resurrection from among [the] dead, neither marry nor are given in marriage; (aiōn )
amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba. (aiōn )
36 for neither can they die any more, for they are equal to angels, and are sons of God, being sons of the resurrection.
Kuma ba za su sāke mutuwa ba, gama su kamar mala’iku ne. Su’ya’yan Allah ne, tun da su’ya’yan tashin matattu ne.
37 But that the dead rise, even Moses shewed in [the section of] the bush, when he called [the] Lord the God of Abraham and the God of Isaac and the God of Jacob;
Amma bisa ga labari na bishiya nan, mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, ko Musa ma, ya nuna cewa, matattu suna tashi. Gama ya kira Ubangiji, ‘Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yaƙub.’
38 but he is not God of [the] dead but of [the] living; for all live for him.
Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”
39 And some of the scribes answering said, Teacher, thou hast well spoken.
Sai waɗansu malaman dokoki suka amsa suka ce, “Ka faɗi daidai, malam!”
40 For they did not dare any more to ask him anything.
Kuma ba wanda ya sami ƙarfin halin yin masa waɗansu tambayoyi.
41 And he said to them, How do they say that the Christ is David's son,
Sai Yesu ya ce musu, “Yaya suke cewa, ‘Kiristi ɗan Dawuda ne?’
42 and David himself says in the book of Psalms, The Lord said to my Lord, Sit at my right hand
Dawuda da kansa ya faɗa a cikin Zabura, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
43 until I put thine enemies [as] footstool of thy feet?
sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
44 David therefore calls him Lord, and how is he his son?
Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji.’ Ta, yaya zai zama ɗansa?”
45 And, as all the people were listening, he said to his disciples,
Yayinda dukan mutane suna cikin sauraronsa, sai Yesu ya ce wa almajiransa,
46 Beware of the scribes, who like to walk about in long robes, and who love salutations in the market-places, and first seats in the synagogues, and first places at suppers;
“Ku yi hankali da malaman dokoki. Sukan so sa manyan riguna suna zaga, suna sha’awan karɓan gaisuwa a wuraren kasuwanci, da kuma wuraren zama mafi daraja a majami’u, da wuraren bangirma a bukukkuwa.
47 who devour the houses of widows, and as a pretext make long prayers. These shall receive a severer judgment.
Suna mamaye gidajen gwauraye, kuma don burga, suna dogayen addu’o’i. Ga irin waɗannan mutane, za a yi musu hukunci mai tsanani sosai.”