< Lamentations 3 >

1 I am the man that hath seen affliction by the rod of his wrath.
Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
2 Me hath he led, and brought into darkness, and not into light.
Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
3 Surely against me hath he turned again and again his hand all the day.
ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
4 My flesh and my skin hath he wasted away, he hath broken my bones.
Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
5 He hath built against me, and encompassed [me] with gall and toil.
Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
6 He hath made me to dwell in dark places as those that have been long dead.
Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
7 He hath hedged me about that I cannot get out: he hath made my chain heavy.
Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
8 Even when I cry and shout, he shutteth out my prayer.
Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
9 He hath inclosed my ways with hewn stone, he hath made my paths crooked.
Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
10 He is unto me [as] a bear lying in wait, a lion in secret places.
Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
11 He hath turned aside my ways, and pulled me in pieces; he hath made me desolate.
ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
12 He hath bent his bow, and set me as a mark for the arrow.
Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
13 He hath caused the arrows of his quiver to enter into my reins.
Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
14 I am become a derision to all my people; their song all the day.
Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
15 He hath sated me with bitterness, he hath made me drunk with wormwood.
Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
16 He hath also broken my teeth with gravel stones, he hath covered me with ashes.
Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
17 And thou hast removed my soul far off from peace: I have forgotten prosperity.
An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
18 And I said, My strength is perished, and my hope in Jehovah.
Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
19 Remember thou mine affliction and my wandering, the wormwood and the gall.
Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
20 My soul hath [them] constantly in remembrance, and is humbled in me.
Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
21 — This I recall to heart, therefore have I hope.
Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
22 It is of Jehovah's loving-kindness we are not consumed, because his compassions fail not;
Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
23 they are new every morning: great is thy faithfulness.
Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
24 Jehovah is my portion, saith my soul; therefore will I hope in him.
Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
25 Jehovah is good unto them that wait for him, to the soul [that] seeketh him.
Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
26 It is good that one should both wait, and that in silence, for the salvation of Jehovah.
yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
27 It is good for a man that he bear the yoke in his youth:
Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
28 He sitteth solitary and keepeth silence, because he hath laid it upon him;
Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
29 he putteth his mouth in the dust, if so be there may be hope;
Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
30 he giveth his cheek to him that smiteth him; he is filled full with reproach.
Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
31 For the Lord will not cast off for ever;
Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
32 but if he have caused grief, he will have compassion according to the multitude of his loving-kindnesses:
Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
33 for he doth not willingly afflict or grieve the children of men.
Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
34 To crush under foot all the prisoners of the earth,
Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
35 to turn aside the right of a man before the face of the Most High,
ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
36 to wrong a man in his cause, — will not the Lord see it?
ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
37 Who is he that saith, and there cometh to pass, what the Lord hath not commanded?
Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
38 Out of the mouth of the Most High doth not there proceed evil and good?
Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
39 Wherefore doth a living man complain, a man for the punishment of his sins?
Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
40 Let us search and try our ways, and turn again to Jehovah.
Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
41 Let us lift up our heart with [our] hands unto God in the heavens.
Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
42 We have transgressed and have rebelled: thou hast not pardoned.
“Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
43 Thou hast covered thyself with anger, and pursued us; thou hast slain, thou hast not spared.
“Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
44 Thou hast covered thyself with a cloud, that prayer should not pass through.
Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
45 Thou hast made us the offscouring and refuse in the midst of the peoples.
Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
46 All our enemies have opened their mouth against us.
“Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
47 Fear and the pit are come upon us, devastation and ruin.
Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
48 Mine eye runneth down with streams of water for the ruin of the daughter of my people.
Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
49 Mine eye poureth down, and ceaseth not, without any intermission,
Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
50 till Jehovah look down and behold from the heavens.
Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
51 Mine eye affecteth my soul, because of all the daughters of my city.
Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
52 They that are mine enemies without cause have chased me sore like a bird.
Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
53 They have cut off my life in a pit, and cast a stone upon me.
Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
54 Waters streamed over my head; I said, I am cut off.
ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
55 I called upon thy name, Jehovah, out of the lowest pit.
Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
56 Thou hast heard my voice: hide not thine ear at my sighing, at my cry.
Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
57 Thou drewest near in the day that I called upon thee; thou saidst, Fear not.
Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
58 Lord, thou hast pleaded the cause of my soul, thou hast redeemed my life.
Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
59 Jehovah, thou hast seen my wrong: judge thou my cause.
Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
60 Thou hast seen all their vengeance, all their imaginations against me.
Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
61 Thou hast heard their reproach, O Jehovah, all their imaginations against me;
Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
62 the lips of those that rise up against me and their meditation against me all the day.
Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
63 Behold thou their sitting down and their rising up: I am their song.
Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
64 Render unto them a recompence, O Jehovah, according to the work of their hands;
Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
65 give them obduracy of heart, thy curse unto them;
Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
66 pursue them in anger, and destroy them from under the heavens of Jehovah.
Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.

< Lamentations 3 >