< John 9 >
1 And as he passed on, he saw a man blind from birth.
Da Yesu yana wucewa, sai ya ga wani mutum makaho tun daga haihuwa.
2 And his disciples asked him, saying, Rabbi, who sinned, this [man] or his parents, that he should be born blind?
Sai almajiransa suka tambaye shi, “Mallam, wa yayi zunubi, mutumin ne ko iyayensa, har aka haife shi makaho?”
3 Jesus answered, Neither has this [man] sinned nor his parents, but that the works of God should be manifested in him.
Yesu ya amsa, Ba mutumin ne ko iyayensa suka yi zunubi ba, amma domin aikin Allah ya bayyana a cikinsa.
4 I must work the works of him that has sent me while it is day. [The] night is coming, when no one can work.
Dole mu yi aikin wanda ya aiko ni tunda rana. Dare na zuwa inda ba mai iya yin aiki.
5 As long as I am in the world, I am [the] light of the world.
Yayinda ina duniya, ni ne hasken duniya.”
6 Having said these things, he spat on the ground and made mud of the spittle, and put the mud, as ointment, on his eyes.
Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, ya tofa yawu a kasa, ya kwaba kasar da yawunsa, sai ya shafe idanun mutumin da kasar.
7 And he said to him, Go, wash in the pool of Siloam, which is interpreted, Sent. He went therefore and washed, and came seeing.
Ya ce masa, tafi, ka wanke a tafkin Siloam (ma'anarsa: aike).” Sai mutumin ya tafi, ya wanke, ya dawo yana gani.
8 The neighbours therefore, and those who used to see him before, that he was a beggar, said, Is not this he that was sitting and begging?
Sai makwabtansa da mutanen da da suka gan shi tun can yana roko suka ce, “Ba wannan mutum ne wanda ya ke zaune yana roko ba?”
9 Some said, It is he; others said, No, but he is like him: he said, It is I.
Wadansu suka ce, “shi ne.” Wadansu suka ce, “A'a, amma yana kama da shi.” Amma shi ya ce, “Ni ne wannan mutum.”
10 They said therefore to him, How have thine eyes been opened?
Suka ce masa, “To yaya aka bude maka idanu?”
11 He answered [and said], A man called Jesus made mud and anointed mine eyes, and said to me, Go to Siloam and wash: and having gone and washed, I saw.
Sai ya amsa, “Mutumin da ake ce da shi Yesu shi ya kwaba kasa ya shafa mani a idanuna ya ce mani, 'je ka kogin Siluwam ka wanke.' Sai naje na wanke, sannan na samu gani.”
12 They said therefore to him, Where is he? He says, I do not know.
Suka ce masa, “Ina yake?” Ya amsa, “Ban sani ba.”
13 They bring him who was before blind to the Pharisees.
Suka kawo mutumnin da yake makaho a da wurin farisawa.
14 Now it was sabbath when Jesus made the mud and opened his eyes.
A ranar asabar ne kwa Yesu ya kwaba kasa ya bude masa idanu.
15 The Pharisees therefore also again asked him how he received his sight. And he said to them, He put mud upon mine eyes, and I washed, and I see.
Har yanzu farisawan suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Ya ce masu, “Ya sa mani kasa a idanuna, na wanke, kuma yanzu ina gani.”
16 Some of the Pharisees therefore said, This man is not of God, for he does not keep the sabbath. Others said, How can a sinful man perform such signs? And there was a division among them.
Wadansu daga cikin farisawa suka ce, “Wannan mutum ba daga Allah yake ba domin ba ya kiyaye ranar Asabar. “Wadansu suka ce, “Yaya mai zunubi zai yi irin wadannan alamu?” Sai rabuwa ta shiga tsakanin su.
17 They say therefore again to the blind [man], What dost thou say of him, that he has opened thine eyes? And he said, He is a prophet.
Sai suka tambayi makahon kuma, “Me kake cewa game da shi dashike ya bude maka idanu?” Makahon ya ce, “shi annabi ne.”
18 The Jews therefore did not believe concerning him that he was blind and had received sight, until they had called the parents of him that had received sight.
Har yanzu kam Yahudawan basu yarda da makantarsa ba da ganin gari da ya samu, sai da suka kirayo iyayen shi wanda ya sami ganin garin.
19 And they asked them saying, This is your son, of whom ye say that he was born blind: how then does he now see?
Su ka tambayi iyayen, “Wannan shine yaronku da kuka ce an haife shi makaho? Yaya yanzu ya ke iya gani?”
20 His parents answered [them] and said, We know that this is our son, and that he was born blind;
Sai iyayen suka amsa masu, “Mun san wannan yaronmu ne kuma a makaho aka haife shi.
21 but how he now sees we do not know, or who has opened his eyes we do not know. He is of age: ask him; he will speak concerning himself.
Yadda ya ke gani yanzu, bamu sani ba, kuma wanda ya bude masa idanu, bamu sani ba. Ku tambaye shi, ba yaro ba ne. Zai iya magana don kansa.”
22 His parents said these things because they feared the Jews, for the Jews had already agreed that if any one confessed him [to be the] Christ, he should be excommunicated from the synagogue.
Iyayensa sun fadi wadannan abubuwan, domin suna ji tsoron Yahudawan. Gama Yahudiyawan sun rigaya sun yarda duk wanda yace Yesu Almasihu ne, za a fitar dashi daga majami'a.
23 On this account his parents said, He is of age: ask him.
Domin wannan ne, iyayensa suka ce, “Ai shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
24 They called therefore a second time the man who had been blind, and said to him, Give glory to God: we know that this man is sinful.
Suka sake kiran mutumin dake makaho karo na biyu, suka ce masa, “Ka girmama Allah. Mu kam mun sani wannan mutum mai zunubi ne.”
25 He answered therefore, If he is sinful I know not. One thing I know, that, being blind [before], now I see.
Sai wannan mutum ya amsa, “Ban sani ba ko shi mai zunubi ne. Abu guda daya na sani: da Ni makaho ne, amma yanzu ina gani.”
26 And they said to him again, What did he do to thee? how opened he thine eyes?
Sai su ka ce masa, “Me ya yi maka? Ta yaya ya bude idanunka?”
27 He answered them, I told you already and ye did not hear: why do ye desire to hear again? do ye also wish to become his disciples?
Ya amsa, “Na rigaya na gaya maku, amma ba ku ji ba! Don me kuke so ku sake ji? Ko kuma kuna so ku zama almajiransa, haka ne?
28 They railed at him, and said, Thou art his disciple, but we are disciples of Moses.
Sai suka kwabe shi suka ce, “kai ne almajirinsa, amma mu almajiran Musa ne.
29 We know that God spoke to Moses; but [as to] this [man], we know not whence he is.
Mun sani Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum, bamu san ko daga ina ne ya zo ba.”
30 The man answered and said to them, Now in this is a wonderful thing, that ye do not know whence he is, and he has opened mine eyes.
Mutumin ya amsa masu ya ce, “Tirkashi, baku san inda ya fito ba, duk da haka shi ya bude mani idanu.
31 [But] we know that God does not hear sinners; but if any one be God-fearing and do his will, him he hears.
Mun san da cewa Allah baya jin masu zunubi, amma idan wani mai ibada ne yana kuma yin nufinsa, to yana jin sa.
32 Since time was, it has not been heard that any one opened the eyes of one born blind. (aiōn )
Tunda duniya ta fara ba a taba jin cewa wani ya bude idanun wanda aka haifa makaho ba. (aiōn )
33 If this [man] were not of God he would be able to do nothing.
In mutumin nan ba daga Allah yake ba, ba zai iya yin komai ba.”
34 They answered and said to him, Thou hast been wholly born in sins, and thou teachest us? And they cast him out.
Suka amsa suka ce masa, “an haife ka cikin zunubai, yanzu kana so ka yi mana koyarwa?” Sai suka fitar da shi.
35 Jesus heard that they had cast him out, and having found him, he said to him, Thou, dost thou believe on the Son of God?
Yesu ya ji cewa sun fitar da shi daga majami'a. Da ya same shi sai ya ce masa, “Kana bada gaskiya ga Dan Allah?”
36 He answered and said, And who is he, Lord, that I may believe on him?
Sai ya amsa masa yace, “Wanene shi, Ubangiji, da zan bada gaskiya gare shi?”
37 And Jesus said to him, Thou hast both seen him, and he that speaks with thee is he.
Yesu yace masa, “Ai ka gan shi, shine wanda yake magana da kai.”
38 And he said, I believe, Lord: and he did him homage.
Mutumin ya ce, “Ubangiji, Na bada gaskiya.” Sai ya yi masa sujada.
39 And Jesus said, For judgment am I come into this world, that they which see not may see, and they which see may become blind.
Yesu ya ce, “Don hukunci na zo wannan duniya domin wadanda ba su gani su gani, saboda kuma wadanda suke gani su zama makafi.”
40 And [some] of the Pharisees who were with him heard these things, and they said to him, Are we blind also?
Wadansu Farisawa wadanda suke tare da shi suka ji wadannan abubuwan, suka tambaye shi, “Muma makafi ne?”
41 Jesus said to them, If ye were blind ye would not have sin; but now ye say, We see, your sin remains.
Yesu ya ce masu, “Inda ku makafi ne, da ba ku da zunubi, amma yanzu kun ce, 'Muna gani', don haka zunubinku ya tabbata.