< John 4 >

1 When therefore the Lord knew that the Pharisees had heard that Jesus makes and baptises more disciples than John
Da Yesu ya sani cewa Farisawa sun ji cewa yana samun almajirai yana kuma yi masu baftisma fiye da Yahaya
2 (however, Jesus himself did not baptise, but his disciples),
(ko da shike ba Yesu da kansa ke yin baftismar ba, amma almajiransa ne),
3 he left Judaea and went away again unto Galilee.
ya bar Yahudiya ya koma Galili.
4 And he must needs pass through Samaria.
Amma ya zamar masa dole ya ratsa ta Samariya.
5 He comes therefore to a city of Samaria called Sychar, near to the land which Jacob gave to his son Joseph.
Ya zo wani birnin Samariya, mai suna Sika, kusa da filin da Yakubu ya ba dansa Yusufu.
6 Now a fountain of Jacob's was there; Jesus therefore, being wearied with the way he had come, sat just as he was at the fountain. It was about the sixth hour.
Rijiyar Yakubu na wurin. Da Yesu ya gaji da tafiyarsa sai ya zauna gefen rijiyar. Kusan karfe goma sha biyu na rana ne.
7 A woman comes out of Samaria to draw water. Jesus says to her, Give me to drink
Wata mace, Ba-Samariya ta zo domin ta dibi ruwa, sai Yesu ya ce mata, “Ba ni ruwa in sha.”
8 (for his disciples had gone away into the city that they might buy provisions).
Gama almajiransa sun tafi cikin gari don sayen abinci.
9 The Samaritan woman therefore says to him, How dost thou, being a Jew, ask to drink of me who am a Samaritan woman? for Jews have no intercourse with Samaritans.
Sai ba-Samariyar tace masa, “Yaya kai da kake Bayahude kake tambaya ta ruwan sha, ni da nike 'yar Samariya?” Domin Yahudawa ba su harka da Samariyawa.
10 Jesus answered and said to her, If thou knewest the gift of God, and who it is that says to thee, Give me to drink, thou wouldest have asked of him, and he would have given thee living water.
Sai Yesu ya amsa yace mata, “In da kin san kyautar Allah, da shi wanda yake ce da ke, 'Ba ni ruwan sha,' da kin roke shi, sai kuma ya ba ki ruwan rai.”
11 The woman says to him, Sir, thou hast nothing to draw with, and the well is deep: whence then hast thou the living water?
Matar tace masa, “Mallam, ga shi ba ka da guga, kuma rijiyar tana da zurfi. Ina za ka samu ruwan rai?
12 Art thou greater than our father Jacob, who gave us the well, and drank of it himself, and his sons, and his cattle?
Ai ba ka fi Ubanmu Yakubu ba, ko ka fi shi, shi wanda ya ba mu rijiyar, shi kansa kuma ya sha daga cikin ta, haka kuma 'ya'yansa da shanunsa?”
13 Jesus answered and said to her, Every one who drinks of this water shall thirst again;
Yesu ya amsa yace mata, “duk wanda ya sha daga wannan ruwan zai sake jin kishi,
14 but whosoever drinks of the water which I shall give him shall never thirst for ever, but the water which I shall give him shall become in him a fountain of water, springing up into eternal life. (aiōn g165, aiōnios g166)
amma duk wanda ya sha daga ruwa da zan ba shi ba zai sake jin kishi ba. Maimakon haka, ruwan da zan bashi zai zama mabulbular ruwa a cikinsa wanda ke bulbula zuwa rai madawwami.” (aiōn g165, aiōnios g166)
15 The woman says to him, Sir, give me this water, that I may not thirst nor come here to draw.
Matar tace masa, “Mallam, ka ba ni wannan ruwa yadda ba zan kara jin kishi ba ba kuma sai na zo nan don in dibi ruwa ba.”
16 Jesus says to her, Go, call thy husband, and come here.
Yesu ya ce mata, “Je, ki kira maigidanki ku zo nan tare.”
17 The woman answered and said, I have not a husband. Jesus says to her, Thou hast well said, I have not a husband;
Matar ta amsa tace masa, “Ba ni da miji.” Yesu yace, “Kin fadi daidai da kika ce, 'ba ni da miji,'
18 for thou hast had five husbands, and he whom now thou hast is not thy husband: this thou hast spoken truly.
domin kin auri mazaje har biyar, kuma wanda kike da shi yanzu ba mijin ki bane. Abinda kika fada gaskiya ne.”
19 The woman says to him, Sir, I see that thou art a prophet.
Matar tace masa, “Mallam, Na ga kai annabi ne.
20 Our fathers worshipped in this mountain, and ye say that in Jerusalem is the place where one must worship.
Ubaninmu sun yi sujada a wannan dutse, amma kun ce Urushalima ce wurin da ya kamata mutane su yi sujada.”
21 Jesus says to her, Woman, believe me, [the] hour is coming when ye shall neither in this mountain nor in Jerusalem worship the Father.
Yesu ya ce mata, “Mace, ki gaskata ni, cewa lokaci na zuwa wanda ba za ku yi wa Uban sujada ba ko akan wannan dutse ko a Urushalima.
22 Ye worship ye know not what; we worship what we know, for salvation is of the Jews.
Ku kuna bauta wa abinda ba ku sani ba. Mu muna bauta wa abinda muka sani, gama ceto daga Yahudawa yake.
23 But [the] hour is coming and now is, when the true worshippers shall worship the Father in spirit and truth; for also the Father seeks such as his worshippers.
Sai dai, sa'a tana zuwa, har ma ta yi, wadda masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a cikin ruhu da gaskiya, domin irin wadannan ne Uban ke nema su zama masu yi masa sujada.
24 God [is] a spirit; and they who worship him must worship [him] in spirit and truth.
Allah Ruhu ne, kuma mutanen da ke yi masa sujada, dole su yi sujada cikin ruhu da gaskiya.”
25 The woman says to him, I know that Messias is coming, who is called Christ; when he comes he will tell us all things.
Matar ta ce masa, “Na san Almasihu na zuwa (wanda ake kira Kristi). Sa'adda ya zo, zai bayyana mana kowane abu.
26 Jesus says to her, I who speak to thee am [he].
Yesu ya ce mata, “Ni ne shi, wanda ke yi maki magana.”
27 And upon this came his disciples, and wondered that he spoke with a woman; yet no one said, What seekest thou? or, Why speakest thou with her?
A daidai wannan lokaci, almajiransa suka dawo. Suna ta mamakin dalilin da yasa yake magana da mace, amma babu wanda yace, “Me kake so?” Ko kuma, “Don me ka ke magana da ita?”
28 The woman then left her waterpot and went away into the city, and says to the men,
Sai matar ta bar tulunta, ta koma cikin gari, tace wa mutanen,
29 Come, see a man who told me all things I had ever done: is not he the Christ?
“Ku zo ku ga wani mutum wanda ya gaya mani duk wani abu da na taba yi. Wannan dai ba Almasihun bane, ko kuwa?”
30 They went out of the city and came to him.
Suka bar garin suka zo wurinsa.
31 But meanwhile the disciples asked him saying, Rabbi, eat.
A wannan lokacin, almajiransa suna rokansa, cewa, “Mallam, ka ci.”
32 But he said to them, I have food to eat which ye do not know.
Amma ya ce masu, “ina da abinci da ba ku san komai akai ba.”
33 The disciples therefore said to one another, Has any one brought him [anything] to eat?
Sai almajiran suka ce da junansu, “Babu wanda ya kawo masa wani abu ya ci, ko akwai ne?”
34 Jesus says to them, My food is that I should do the will of him that has sent me, and that I should finish his work.
Yesu ya ce masu, “Abincina shine in yi nufin wanda ya aiko ni, in kuma cika aikinsa.
35 Do not ye say, that there are yet four months and the harvest comes? Behold, I say to you, Lift up your eyes and behold the fields, for they are already white to harvest.
Ba ku kan ce, 'akwai wata hudu tukuna kafin girbi ya zo ba?' Ina gaya maku, daga idanunku ku ga gonakin, sun rigaya sun isa girbi.
36 He that reaps receives wages and gathers fruit unto life eternal, that both he that sows and he that reaps may rejoice together. (aiōnios g166)
Shi wanda ke girbi yakan karbi sakamako ya kuma tattara amfanin gona zuwa rai na har abada, ta haka shi mai shuka da shi mai girbi za su yi farinciki tare. (aiōnios g166)
37 For in this is [verified] the true saying, It is one who sows and another who reaps.
Gama cikin wannan maganar take, 'Wani na shuka, wani kuma na girbi.'
38 I have sent you to reap that on which ye have not laboured; others have laboured, and ye have entered into their labours.
Na aike ku ku yi girbin abinda ba ku yi aiki a kai ba. Wandansu sun yi aiki, ku kuma kun shiga cikin wahalarsu.
39 But many of the Samaritans of that city believed on him because of the word of the woman who bore witness, He told me all things that I had ever done.
Yawancin Samariyawan da ke wannan birni suka gaskata da shi sabili da labarin matar data bada shaida, “Ya gaya mani duk abinda na taba yi.”
40 When therefore the Samaritans came to him they asked him to abide with them, and he abode there two days.
To sa'adda Samariyawa suka zo wurinsa, sai suka roke shi ya zauna tare da su, ya kuwa zauna wurin kwana biyu.
41 And more a great deal believed on account of his word;
Wasu da dama kuma suka gaskata domin maganarsa.
42 and they said to the woman, [It is] no longer on account of thy saying that we believe, for we have heard him ourselves, and we know that this is indeed the Saviour of the world.
Suka cewa matar, “Mun bada gaskiya, ba saboda maganar ki kadai ba, amma mu kanmu munji, yanzu kuma mun sani cewa wannan lallai shine mai ceton duniya.”
43 But after the two days he went forth thence and went away into Galilee,
Bayan wadannan kwana biyu, ya bar wurin zuwa Galili.
44 for Jesus himself bore witness that a prophet has no honour in his own country.
Domin Yesu da kansa yace, ba a girmama annabi a kasarsa.
45 When therefore he came into Galilee, the Galileans received him, having seen all that he had done in Jerusalem during the feast, for they also went to the feast.
Da ya zo Galili, Galiliyawan suka marabce shi. Sun ga dukan abubuwan da ya yi a Urushalima wurin idin, domin su ma sun je idin.
46 He came therefore again to Cana of Galilee, where he made the water wine. And there was a certain courtier in Capernaum whose son was sick.
Kuma ya koma Kana ta Galili inda ya mayar da ruwa zuwa ruwan inabi. Akwai wani ma'aikacin fada wanda dansa na rashin lafiya a Kafarnahum.
47 He, having heard that Jesus had come out of Judaea into Galilee, went to him and asked [him] that he would come down and heal his son, for he was about to die.
Da ya ji cewa Yesu ya bar Yahudiya ya koma Galili, sai ya tafi wurin Yesu ya roke shi ya sauko ya warka da dansa wanda ke bakin mutuwa.
48 Jesus therefore said to him, Unless ye see signs and wonders ye will not believe.
Yesu yace masa, “Idan ba ku ga alamu da mu'ujizai ba, ba za ku gaskata ba.”
49 The courtier says to him, Sir, come down ere my child die.
Ma'aikacin ya ce masa, “Mallam, ka sauko kafin da na ya mutu.”
50 Jesus says to him, Go, thy son lives. And the man believed the word which Jesus said to him, and went his way.
Yesu yace masa, “Je ka. Dan ka ya rayu.” Mutumin ya gaskata maganar da Yesu ya gaya masa, Sai yayi tafiyarsa.
51 But already, as he was going down, his servants met him and brought [him] word saying, Thy child lives.
Yayin da yake sauka kasa, bayinsa suka same shi, suna cewa, danka yana raye.
52 He inquired therefore from them the hour at which he got better. And they said to him, Yesterday at the seventh hour the fever left him.
Sai ya tambaye su sa'ar da ya fara samun sauki. Suka amsa masa, “Jiya a sa'a ta bakwai zazabin ya bar shi.”
53 The father therefore knew that [it was] in that hour in which Jesus said to him, Thy son lives; and he believed, himself and his whole house.
Sai Uban ya gane cewa wannan sa'a ce Yesu ya ce masa, “Jeka, danka na raye.” Sabili da haka, shi da dukan gidansa suka bada gaskiya.
54 This second sign again did Jesus, being come out of Judaea into Galilee.
Wannan ce alama ta biyu da Yesu ya yi bayan da ya bar Yahudiya zuwa Galili.

< John 4 >