< John 2 >

1 And on the third day a marriage took place in Cana of Galilee, and the mother of Jesus was there.
Bayan kwana uku, akwai aure a Kana ta Galili, mahaifiyar Yesu kuma tana wurin.
2 And Jesus also, and his disciples, were invited to the marriage.
An gayyaci Yesu da almajiransa zuwa auren.
3 And wine being deficient, the mother of Jesus says to him, They have no wine.
Da ruwan inabin ya kare, maihafiyar Yasu tace masa, “basu da ruwan inabi.”
4 Jesus says to her, What have I to do with thee, woman? mine hour has not yet come.
Yesu yace mata, “Mace, me yasa kika zo wurina? Lokaci na bai yi ba tukuna”.
5 His mother says to the servants, Whatever he may say to you, do.
Maihafiyarsa tace wa ma'aikatan, “Ku yi duk abin da yace maku.”
6 Now there were standing there six stone water-vessels, according to the purification of the Jews, holding two or three measures each.
To akwai randunan ruwa na dutse guda shidda a wurin wadanda Yahudawa ke amfani da su domin al'adansu na tsarkakewa, kowace zata iya daukar durom guda.
7 Jesus says to them, Fill the water-vessels with water. And they filled them up to the brim.
Yesu yace masu, “Cika randunan da ruwa”. Sai suka cika randunan makil.
8 And he says to them, Draw out now, and carry [it] to the feast-master. And they carried [it].
Sai yace wa ma'aikatan, “Ku diba daga ciki ku kai wa shugaban biki.” Sai suka yi hakannan.
9 But when the feast-master had tasted the water which had been made wine (and knew not whence it was, but the servants knew who drew the water), the feast-master calls the bridegroom,
Shugaban bikin ya dandana ruwan da ya zama ruwan inabin, amma bai san inda ya fito ba (amma ma'aikatan wadanda suka jawo ruwan sun sani). Sai ya kira ango
10 and says to him, Every man sets on first the good wine, and when [men] have well drunk, then the inferior; thou hast kept the good wine till now.
yace masa, “Kowane mutum yakan raba ruwan inabi mai kyau da farko, kafin mai arhar bayan an shanye mai kyaun. Amma kai ka ajiye mai kyaun sai yanzu.”
11 This beginning of signs did Jesus in Cana of Galilee, and manifested his glory; and his disciples believed on him.
Wannan alama ta farko ce da Yesu yayi a Kana ta Galili, ya kuma bayyana daukakarsa, almajiransa kuma suka gaskata da shi.
12 After this he descended to Capernaum, he and his mother and his brethren and his disciples; and there they abode not many days.
Bayan wannan, Yesu, da mahaifiyarsa, da 'yan'uwansa da almajiransa suka tafi Kafarnahum, kuma suka zauna can wasu 'yan kwanaki.
13 And the passover of the Jews was near, and Jesus went up to Jerusalem.
To idin ketarewa na Yahudawa ya kusato, Yesu kuwa ya wuce zuwa Urushalima.
14 And he found in the temple the sellers of oxen and sheep and doves, and the money-changers sitting;
Ya iske wadanda suke sayar da shanu da tumaki da tantabaru, masu canjin kudi kuma na zaune a wurin.
15 and, having made a scourge of cords, he cast [them] all out of the temple, both the sheep and the oxen; and he poured out the change of the money-changers, and overturned the tables,
Sai yayi tsumingiya da igiyoyi ya kore su duka daga cikin haikalin, duk da tumakin da shanun. Sai ya watsar da sulallan masu canjin kudin ya birkitar da teburansu.
16 and said to the sellers of doves, Take these things hence; make not my Father's house a house of merchandise.
Yace wa masu sayar da tantabaru, “Ku fitar da wadannan abubuwa daga nan. Ku daina maida gidan Ubana wurin kasuwanci.”
17 [And] his disciples remembered that it is written, The zeal of thy house devours me.
Almajiransa suka tuna a rubuce yake, “Himma domin gidanka za ta cinye ni.”
18 The Jews therefore answered and said to him, What sign shewest thou to us, that thou doest these things?
Sai shugabannin Yahudawa suka amsa suka ce masa, “Wace alama za ka nuna mana, da shike kana yin wadannan abubuwan?”
19 Jesus answered and said to them, Destroy this temple, and in three days I will raise it up.
Yesu ya amsa, “Ku rushe wannan haikali, kuma a cikin kwana uku zan gina shi.”
20 The Jews therefore said, Forty and six years was this temple building, and thou wilt raise it up in three days?
Sai shugabanin Yahudawa suka ce, “An dauki shekaru arba'in da shidda kamin a gama gina wannan haikalin, za ka dau kwanaki uku kadai wajen gina shi?”
21 But he spoke of the temple of his body.
Amma yana nufin haikali na jikinsa ne.
22 When therefore he was raised from among [the] dead, his disciples remembered that he had said this, and believed the scripture and the word which Jesus had spoken.
Bayan da aka tashe shi daga matattu, sai almajiransa suka tuna ya fadi haka, suka kuma ba da gaskiya ga nassi da wannan kalami da Yesu ya fada.
23 And when he was in Jerusalem, at the passover, at the feast, many believed on his name, beholding his signs which he wrought.
Kuma, da yana Urushalima a idin ketarewa, a lokacin idin, mutane da yawa suka gaskata ga sunansa, sa'adda suka ga alamun da ya yi.
24 But Jesus himself did not trust himself to them, because he knew all [men],
Amma Yesu bai yadda da su ba domin ya san su duka,
25 and that he had not need that any should testify of man, for himself knew what was in man.
saboda baya bukatar wani ya shaida masa game da mutum, domin ya san abinda ke cikin sa.

< John 2 >