< John 15 >
1 I am the true vine, and my Father is the husbandman.
“Nine itacen inabi na hakika, Ubana kuwa shi ne manomin.
2 [As to] every branch in me not bearing fruit, he takes it away; and [as to] every one bearing fruit, he purges it that it may bring forth more fruit.
Yakan cire duk wani rashe a cikina da ba ya bada 'ya'ya, mai bada 'ya'ya kuwa ya kan gyara shi domin ya kara bada 'ya'ya.
3 Ye are already clean by reason of the word which I have spoken to you.
Kun rigaya kun tsarkaka saboda maganar da na yi muku.
4 Abide in me and I in you. As the branch cannot bear fruit of itself unless it abide in the vine, thus neither [can] ye unless ye abide in me.
Ku zauna ciki na, Ni kuma cikin ku. Kamar yadda reshe ba ya iya bada 'ya'ya shi kadai sai ya zauna cikin itacen, haka kuma ba za ku iya ba, sai kun zauna ciki na.
5 I am the vine, ye [are] the branches. He that abides in me and I in him, he bears much fruit; for without me ye can do nothing.
Ni ne itacen inabi, ku ne rassan. Wanda ya zauna ciki na, ni kuma cikin sa, yana bada 'ya'ya dayawa, gama in ba tare da ni ba, ba za ku iya yin kome ba.
6 Unless any one abide in me he is cast out as the branch, and is dried up; and they gather them and cast them into the fire, and they are burned.
Wanda kuma bai zauna a ciki na ba, akan jefar da shi kamar reshe, ya bushe, kuma sukan tattara rassan su jefa a wuta, su kone.
7 If ye abide in me, and my words abide in you, ye shall ask what ye will and it shall come to pass to you.
In kun zauna a ciki na, maganata kuma ta zauna a cikin ku, sai ku roki duk abinda kuke so, za a kuwa yi maku.
8 In this is my Father glorified, that ye bear much fruit, and ye shall become disciples of mine.
Ta haka ake daukaka Ubana: cewa ku bada 'ya'ya dayawa, kuma cewa ku almajiraina ne.
9 As the Father has loved me, I also have loved you: abide in my love.
Kamar yadda Ubana ya kaunace ni, haka Ni ma na kaunace ku; Ku zauna cikin kaunata.
10 If ye shall keep my commandments, ye shall abide in my love, as I have kept my Father's commandments and abide in his love.
Idan kun kiyaye dokokina, za ku zauna cikin kaunata kamar yadda Na kiyaye dokokin Ubana, na kuma zauna cikin kaunarsa.
11 I have spoken these things to you that my joy may be in you, and your joy be full.
Ina gaya maku wadannan al'amura domin farincikina ya kasance a cikin ku, kuma domin farincikinku ya zama cikakke.
12 This is my commandment, that ye love one another, as I have loved you.
“Wannan shine umarnina, cewa ku kaunaci juna kamar yadda na kaunace ku.
13 No one has greater love than this, that one should lay down his life for his friends.
Babu wanda ke da kaunar da tafi haka, wato ya bada ransa domin abokansa.
14 Ye are my friends if ye practise whatever I command you.
Ku abokaina ne idan kuna yin abubuwan da na umarce ku.
15 I call you no longer bondmen, for the bondman does not know what his master is doing; but I have called you friends, for all things which I have heard of my Father I have made known to you.
Nan gaba ba zan kara ce da ku bayi ba, don bawa bai san abinda Ubangijinsa ke yi ba. Na kira ku abokaina, domin na sanar da ku duk abinda na ji daga wurin Ubana.
16 Ye have not chosen me, but I have chosen you, and have set you that ye should go and [that] ye should bear fruit, and [that] your fruit should abide, that whatsoever ye shall ask the Father in my name he may give you.
Ba ku kuka zabe ni ba, amma Ni ne na zabe ku, na aike ku don ku je ku bada 'ya'ya, 'ya'yanku kuma su tabbata. Wannan ya zama domin duk abinda kuka roki Uba a cikin sunana, zai baku.
17 These things I command you, that ye love one another.
Na baku wannan umarni: domin ku kaunaci juna.
18 If the world hate you, know that it has hated me before you.
In duniya ta ki ku, ku sani cewa ta kini kafin ta ki ku.
19 If ye were of the world, the world would love its own; but because ye are not of the world, but I have chosen you out of the world, on account of this the world hates you.
Da ku na duniya ne, da duniya ta kaunace ku kamar nata. Amma saboda ku ba na duniya bane, na kuma zabe ku daga duniya, don haka duniya take kin ku.
20 Remember the word which I said unto you, The bondman is not greater than his master. If they have persecuted me, they will also persecute you; if they have kept my word, they will keep also yours.
Ku tuna da maganar da na yi muku, 'Bawa ba ya fi Ubangijinsa girma ba.' Idan sun tsananta mani, ku ma za su tsananta maku; Idan sun kiyaye maganata, za su kuma kiyaye maganarku.
21 But they will do all these things to you on account of my name, because they have not known him that sent me.
Za su yi maku duk wadannan abubuwa saboda sunana, don basu san wanda ya aiko ni ba.
22 If I had not come and spoken to them, they had not had sin; but now they have no excuse for their sin.
Da ban zo na yi masu magana ba, da basu da zunubi, amma yanzu, basu da wata hujja don zunubinsu.
23 He that hates me hates also my Father.
Duk wanda ya ki ni ya ki Ubana.
24 If I had not done among them the works which no other one has done, they had not had sin; but now they have both seen and hated both me and my Father.
Da ban yi ayyukan da babu wanda ya taba yinsu a cikin su ba, da basu da zunubi, amma yanzu sun gani, sun kuma ki ni da Ubana duka.
25 But that the word written in their law might be fulfilled, They hated me without a cause.
An yi wannan kuwa domin a cika maganar da ke rubuce a cikin shari'arsu, ' Sun ki ni ba dalili.'
26 But when the Comforter is come, whom I will send to you from the Father, the Spirit of truth who goes forth from with the Father, he shall bear witness concerning me;
Sa'adda Mai Ta'aziya- wanda zan aiko maku daga wurin Uban, wato, Ruhun gaskiya, wanda ke fita daga wurin Uban-ya zo, zai bada shaida a kai na.
27 and ye too bear witness, because ye are with me from [the] beginning.
Ku ma kuna bada shaida saboda kuna tare da ni tun daga farko.