< Job 36 >

1 And Elihu proceeded and said,
Elihu ya ci gaba,
2 Suffer me a little, and I will shew thee that I have yet words for God.
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 I will fetch my knowledge from afar, and will ascribe righteousness to my Creator.
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 For truly my words shall be no falsehood: one perfect in knowledge is with thee.
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 Lo, God is mighty, but despiseth not [any]; mighty in strength of understanding:
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 He saveth not the wicked alive; but he doeth justice to the afflicted.
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 He withdraweth not his eyes from the righteous, but with kings on the throne doth he even set them for ever; and they are exalted.
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 And if, bound in fetters, they be held in cords of affliction,
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 Then he sheweth them their work, and their transgressions, because they have increased.
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 And he openeth their ear to discipline, and commandeth that they return from iniquity.
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 If they hearken and serve [him], they shall accomplish their days in prosperity, and their years in pleasures.
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 But if they hearken not, they shall pass away by the sword, and expire without knowledge.
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 But the godless in heart heap up anger; they cry not when he bindeth them:
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 Their soul dieth in youth, and their life is among the unclean.
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 But he delivereth the afflicted in his affliction, and openeth their ear in [their] oppression.
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 Even so would he have allured thee out of the jaws of distress into a broad place, where there is no straitness; and the supply of thy table [would be] full of fatness.
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 But thou art full of the judgments of the wicked: judgment and justice take hold [on thee].
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 Because there is wrath, [beware] lest it take thee away through chastisement: then a great ransom could not avail thee.
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 Will he esteem thy riches? Not gold, nor all the resources of strength!
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 Desire not the night, when peoples are cut off from their place.
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 Take heed, turn not to iniquity; for this hast thou chosen rather than affliction.
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 Lo, God is exalted in his power: who teacheth as he?
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 Who hath appointed him his way? or who hath said, Thou hast wrought unrighteousness?
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 Remember that thou magnify his work, which men celebrate.
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 All men look at it; man beholdeth [it] afar off.
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 Lo, God is great, and we comprehend [him] not, neither can the number of his years be searched out.
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 For he draweth up the drops of water: they distil in rain from the vapour which he formeth,
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 Which the skies pour down [and] drop upon man abundantly.
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 But can any understand the spreadings of the clouds, [or] the crashing of his pavilion?
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 Lo, he spreadeth his light around him, and covereth the bottom of the sea.
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 For with them he judgeth the peoples; he giveth food in abundance.
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 [His] hands he covereth with lightning, and commandeth it where it is to strike.
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 His thundering declareth concerning him; the cattle even, concerning its coming.
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.

< Job 36 >