< Job 23 >

1 And Job answered and said,
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2 Even to-day is my complaint bitter: my stroke is heavier than my groaning.
“Ko a yau, ina kuka mai zafi; hannunsa yana da nauyi duk da nishin da nake yi.
3 Oh that I knew where I might find him, that I might come to his seat!
Da a ce na san inda zan same shi; da a ce zan iya zuwa wurin da yake zama!
4 I would order the cause before him, and fill my mouth with arguments;
Zan kai damuwata wurinsa in yi gardama da shi.
5 I would know the words he would answer me, and understand what he would say unto me.
Zan nemi in san abin da zai ce mini, in kuma auna abin da zai ce mini.
6 Would he plead against me with [his] great power? Nay; but he would give heed unto me.
Zai yi gardama da ni da ikonsa mai girma? Babu, ba zai zarge ni da laifi ba.
7 There would an upright man reason with him; and I should be delivered for ever from my judge.
Mai adalci ne zai kawo ƙara a wurinsa, kuma zan samu kuɓuta daga wurin mai shari’an nan har abada.
8 Lo, I go forward, but he is not there; and backward, but I do not perceive him;
“Amma in na je gabas, ba ya wurin; in na je yamma, ba zan same shi ba.
9 On the left hand, where he doth work, but I behold [him] not; he hideth himself on the right hand, and I see [him] not.
Sa’ad da yake aiki a arewa, ba ni ganinsa; sa’ad da ya juya zuwa kudu, ba na ganinsa.
10 But he knoweth the way that I take; he trieth me, I shall come forth as gold.
Amma ya san hanyar da nake bi; sa’ad da ya gwada ni zan fito kamar zinariya.
11 My foot hath held to his steps; his way have I kept, and not turned aside.
Ƙafafuna suna bin ƙafafunsa kurkusa; na bi hanyarsa ba tare da na juya ba.
12 Neither have I gone back from the commandment of his lips; I have laid up the words of his mouth more than the purpose of my own heart.
Ban fasa bin dokokin da ya bayar ba; na riƙe maganarsa da muhimmanci fiye da abincin yau da gobe.
13 But he is in one [mind], and who can turn him? And what his soul desireth, that will he do.
“Amma ya tsaya shi kaɗai, kuma wa ya isa yă ja da shi? Yana yin abin da yake so.
14 For he will perform [what] is appointed for me; and many such things are with him.
Yana yi mini abin da ya shirya yă yi mini, kuma yana da sauran irinsu a ajiye.
15 Therefore am I troubled at his presence; I consider, and I am afraid of him.
Shi ya sa na tsorata a gabansa; sa’ad da na yi tunanin wannan duka, nakan ji tsoronsa.
16 For God hath made my heart soft, and the Almighty troubleth me;
Allah ya sa zuciyata ta yi sanyi; Maɗaukaki ya tsorata ni.
17 Because I was not cut off before the darkness, neither hath he hidden the gloom from me.
Duk da haka duhun bai sa in yi shiru ba, duhun da ya rufe mini fuska.

< Job 23 >