< Job 16 >

1 And Job answered and said,
Sai Ayuba ya amsa,
2 I have heard many such things: grievous comforters are ye all.
“Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
3 Shall words of wind have an end? or what provoketh thee that thou answerest?
Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
4 I also could speak as ye: if your soul were in my soul's stead, I could join together words against you, and shake my head at you;
Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
5 [But] I would encourage you with my mouth, and the solace of my lips should assuage [your pain].
Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
6 If I speak, my pain is not assuaged; and if I forbear, what am I eased?
“Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
7 But now he hath made me weary; ...thou hast made desolate all my family;
Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
8 Thou hast shrivelled me up! it is become a witness; and my leanness riseth up against me, it beareth witness to my face.
Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
9 His anger teareth and pursueth me; he gnasheth with his teeth against me; [as] mine adversary he sharpeneth his eyes at me.
Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
10 They gape upon me with their mouth; they smite my cheeks reproachfully; they range themselves together against me.
Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
11 God hath delivered me over to the iniquitous man, and hurled me into the hands of the wicked.
Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
12 I was at rest, but he hath shattered me; he hath taken me by the neck and shaken me to pieces, and set me up for his mark.
Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
13 His arrows encompass me round about, he cleaveth my reins asunder and doth not spare; he poureth out my gall upon the ground.
maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
14 He breaketh me with breach upon breach; he runneth upon me like a mighty man.
Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
15 I have sewed sackcloth upon my skin, and rolled my horn in the dust.
“Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
16 My face is red with weeping, and on my eyelids is the shadow of death;
Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
17 Although there is no violence in my hands, and my prayer is pure.
duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
18 O earth, cover not my blood, and let there be no place for my cry!
“Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
19 Even now, behold, my Witness is in the heavens, and he that voucheth for me is in the heights.
Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
20 My friends are my mockers; mine eye poureth out tears unto God.
Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
21 Oh that there were arbitration for a man with God, as a son of man for his friend!
a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
22 For years [few] in number shall pass, — and I shall go the way [whence] I shall not return.
“Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.

< Job 16 >