< Hebrews 4 >
1 Let us therefore fear, lest, a promise being left of entering into his rest, any one of you might seem to have failed [of it].
Saboda haka, sai muyi lura kwarai don kada wani ya kasa kai ga shiga hutun da aka alkawarta maku na Allah.
2 For indeed we have had glad tidings presented to us, even as they also; but the word of the report did not profit them, not being mixed with faith in those who heard.
Don mun ji albishir game da hutun Allah kamar yadda aka fada masu. Amma wancan sakon bai anfana ga wadanda suka ji ba tare da sun bada gaskiya ga sakon ba.
3 For we enter into the rest who have believed; as he said, As I have sworn in my wrath, If they shall enter into my rest; although the works had been completed from [the] foundation of [the] world.
Ai mu, wadanda muka gaskata-mune zamu shiga wannan hutun, kamar yadda ya ce, “Yadda na yi rantsuwa cikin fushina, baza su shiga hutu na ba.” Ya fadi hakan, ko da yake ya gama aikin hallittarsa tun daga farkon duniya.
4 For he has said somewhere of the seventh [day] thus, And God rested on the seventh day from all his works:
Domin yayi fadi a wani wuri game da rana ta bakwai, “Allah ya huta a rana ta bakwai daga dukkan ayyukansa.”
5 and in this again, If they shall enter into my rest.
Ya sake cewa, “Baza su taba shiga hutu na ba.”
6 Seeing therefore it remains that some enter into it, and those who first received the glad tidings did not enter in on account of not hearkening to the word,
Saboda haka, tun da hutun Allah na kebe domin masu su shiga, kuma tun da Isra'ilawa da yawa wadanda suka ji sakon nan mai kyau game da hutunsa ba su shiga ba saboda rashin biyayya,
7 again he determines a certain day, saying, in David, 'To-day,' after so long a time; (according as it has been said before), To-day, if ye will hear his voice, harden not your hearts.
Allah ya sake shirya wata rana da ake kira, “Yau.” Ya sa wannan rana sa'adda yayi magana ta wurin Dauda, wanda ya ce tun da dadewa da aka fara fada, “Yau idan kun ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku.”
8 For if Jesus had brought them into rest, he would not have spoken afterwards about another day.
Don idan Joshua ya ba su hutu, da Allah ba zai sake magana a kan wata rana ba.
9 There remains then a sabbatism to the people of God.
Saboda haka, akwai hutun asabar kebabbe ga mutanen Allah.
10 For he that has entered into his rest, he also has rested from his works, as God did from his own.
Don shi wanda ya shiga hutun Allah shi kansa ma ya huta daga ayyukansa, kamar yadda Allah yayi da nasa.
11 Let us therefore use diligence to enter into that rest, that no one may fall after the same example of not hearkening to the word.
Saboda haka muyi marmarin shiga wancan hutun, don kada kowa ya fadi ga irin rashin biyayyar da suka yi.
12 For the word of God [is] living and operative, and sharper than any two-edged sword, and penetrating to [the] division of soul and spirit, both of joints and marrow, and a discerner of the thoughts and intents of [the] heart.
Maganar Allah kuwa rayayyiyace, kuma mai ci, fiye da takobi mai kaifi-biyu. Takan ratsa har tsakanin rai da ruhu, kuma tana kaiwa bargo. Takan iya bincika tunanin zuciya da manufarta.
13 And there is not a creature unapparent before him; but all things [are] naked and laid bare to his eyes, with whom we have to do.
Babu halittaccen abu da ke boye a idon Allah. Sai dai, kome a sarari yake, kuma a bayyane yake a idonsa wanda lallai ne zamu bada lissafin kanmu a gare shi.
14 Having therefore a great high priest who has passed through the heavens, Jesus the Son of God, let us hold fast the confession.
Da yake muna da babban firist wanda ya ratsa sammai, Yesu Dan Allah, sai mu riki bangaskiyarmu da karfi.
15 For we have not a high priest not able to sympathise with our infirmities, but tempted in all things in like manner, sin apart.
Domin babban firist namu ba marar tausayi ga kasawarmu bane, amma wanda aka jarraba ne ta ko wanne hali irin yadda aka yi mana, sai dai ba'a same shi da zunubi ba.
16 Let us approach therefore with boldness to the throne of grace, that we may receive mercy, and find grace for seasonable help.
Sai mu zo wurin kursiyin alheri gabagadi, domin a yi mana jinkai mu kuwa sami alherin da zai taimake mu a lokacin bukata.