< Genesis 8 >
1 And God remembered Noah, and all the animals, and all the cattle that were with him in the ark; and God made a wind to pass over the earth, and the waters subsided.
Amma Allah ya tuna da Nuhu da dukan namun jeji da dabbobin da suke tare da shi a cikin jirgi, ya kuma aika da wata iska ta hura dukan duniya, ruwan kuwa ya janye.
2 And the fountains of the deep and the windows of heaven were closed, and the pour of rain from heaven was stopped.
Aka toshe maɓuɓɓugan zurfafa da ƙofofin ambaliyar sammai, ruwan sama kuma ya daina saukowa daga sarari.
3 And the waters retired from the earth, continually retiring; and in the course of a hundred and fifty days the waters abated.
Ruwan ya janye a hankali daga ƙasa. A ƙarshen kwanaki ɗari da hamsin ɗin, ruwan ya ragu.
4 And the ark rested in the seventh month, on the seventeenth day of the month, on the mountains of Ararat.
A rana ta goma sha bakwai ga watan bakwai, jirgin ya sauka a duwatsun Ararat.
5 And the waters abated continually until the tenth month: in the tenth [month], on the first of the month, the tops of the mountains were seen.
Ruwan ya ci gaba da janyewa har watan goma. A rana ta fari ga watan goma kuwa ƙwanƙolin duwatsun suka bayyana.
6 And it came to pass at the end of forty days that Noah opened the window of the ark which he had made.
Bayan kwana arba’in, sai Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi,
7 And he sent out the raven, which went forth going to and fro, until the waters were dried from the earth.
ya saki hankaka. Hankaka ya yi ta kai da kawowa har sai da ruwa ya shanye a duniya.
8 And he sent out the dove from him, to see if the waters had become low on the ground.
Sai ya saki kurciya don yă ga in ruwan ya janye daga doron ƙasa.
9 But the dove found no resting-place for the sole of her foot, and returned to him into the ark; for the waters were on the whole earth; and he put forth his hand, and took her, and brought her to him into the ark.
Amma kurciyar ba tă sami inda za tă sa ƙafafunta ba gama akwai ruwa a dukan doron ƙasa, saboda haka ta komo wurin Nuhu a jirgi. Ya miƙa hannunsa ya ɗauko kurciyar ya shigar da ita wurinsa a cikin jirgi.
10 And he waited yet other seven days, and again he sent forth the dove out of the ark.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar daga jirgi.
11 And the dove came to him at eventide; and behold, in her beak was an olive-leaf plucked off; and Noah knew that the waters had become low on the earth.
Sa’ad da kurciya ta komo wurinsa da yamma, sai ga ɗanyen ganyen zaitun da ta tsinko a bakinta! Sa’an nan Nuhu ya san cewa ruwa ya janye daga duniya.
12 And he waited yet other seven days, and sent forth the dove; but she returned no more to him.
Ya ƙara jira kwana bakwai, sai ya sāke aiken kurciyar, amma a wannan ƙaro ba tă komo wurinsa ba.
13 And it came to pass in the six hundred and first year, in the first [month], on the first of the month, that the waters were dried up from the earth. And Noah removed the covering of the ark, and looked, and behold, the surface of the ground was dried.
A rana ta fari ga wata na fari wanda Nuhu ya cika shekaru 601, ruwa ya shanye a ƙasa. Sai Nuhu ya buɗe murfin jirgin, ya ga cewa doron ƙasa ya bushe.
14 And in the second month, on the twenty-seventh day of the month, the earth was dry.
A ran ashirin da bakwai ga wata na biyu, ƙasa ta bushe ƙaƙaf.
15 And God spoke to Noah, saying,
Sa’an nan Allah ya ce wa Nuhu,
16 Go out of the ark, thou, and thy wife, and thy sons, and thy sons' wives with thee.
“Fito daga jirgin, kai da matarka da’ya’yanka maza da matansu.
17 Bring forth with thee every animal which is with thee, of all flesh, fowl as well as cattle, and all the creeping things which creep on the earth, that they may swarm on the earth, and may be fruitful and multiply on the earth.
Ka fitar da kowane iri halitta mai rai da take tare da kai waje, tsuntsaye, dabbobi, da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa, don su yi ta haihuwa, su yi yawa, su ƙaru a duniya.”
18 And Noah went out, and his sons, and his wife, and his sons' wives with him.
Sai Nuhu ya fito tare da matarsa da’ya’yansa maza da matan’ya’yansa,
19 All the animals, all the creeping things, and all the fowl — everything that moves on the earth, after their kinds, went out of the ark.
da kowace irin dabba, da kowane mai rarrafe, da kowane irin tsuntsu, da kowane irin abu da yake tafiya a bisa duniya, suka fito daga jirgi daki-daki bisa ga irinsu.
20 And Noah built an altar to Jehovah; and took of every clean animal, and of all clean fowl, and offered up burnt-offerings on the altar.
Sai Nuhu ya gina bagaden hadaya ga Ubangiji, ya ɗiba waɗansu dabbobi da tsuntsaye masu tsabta, ya yi hadaya ta ƙonawa da su a kan bagaden.
21 And Jehovah smelled the sweet odour. And Jehovah said in his heart, I will no more henceforth curse the ground on account of Man, for the thought of Man's heart is evil from his youth; and I will no more smite every living thing, as I have done.
Da Ubangiji ya ji ƙanshi mai daɗi, sai ya ce a zuciyarsa, “Ba zan ƙara la’anta ƙasa saboda mutum ba, ko da yake dukan tunanin zuciyar mutum mugu ne tun yana ƙarami. Ba kuwa zan ƙara hallaka dukan halittu masu rai, kamar yadda na yi ba.
22 Henceforth, all the days of the earth, seed [time] and harvest, and cold and heat, and summer and winter, and day and night, shall not cease.
“Muddin duniya tana nan, lokacin shuki da na girbi, lokacin sanyi da na zafi, lokacin damina da na rani, dare da rana ba za su daina ba.”