< Genesis 14 >

1 And it came to pass in the days of Amraphel the king of Shinar, Arioch the king of El-lasar, Chedorlaomer the king of Elam, and Tidal the king of nations,
A zamanin Amrafel sarkin Shinar, shi da Ariyok sarkin Ellasar, Kedorlayomer sarkin Elam, da kuma Tidal sarkin Goyim
2 [that] they made war with Bera the king of Sodom, and with Birsha the king of Gomorrah, Shinab the king of Admah, and Shemeber the king of Zeboim, and the king of Bela, which is Zoar.
suka tafi don su yaƙi Bera sarkin Sodom, Birsha sarkin Gomorra, Shinab sarkin Adma, Shemeber sarkin Zeboyim, da kuma sarkin Bela (wato, Zowar).
3 All these were joined in the vale of Siddim, which is the salt sea.
Dukan waɗannan sarakuna na bayan nan suka haɗa kai a Kwarin Siddim (Teku Gishiri).
4 Twelve years had they served Chedorlaomer; and in the thirteenth year they rebelled.
Shekara goma sha biyu suna bauta wa Kedorlayomer, amma a shekara ta sha uku sai suka yi tawaye.
5 And in the fourteenth year came Chedorlaomer and the kings that were with him, and smote the Rephaim in Ashteroth-karnaim, and the Zuzim in Ham, and the Emim in Shaveh-Kirjathaim,
A shekara ta goma sha huɗu, Kedorlayomer da sarakunan da suka haɗa kai da shi suka tafi suka cinye Refahiyawa a Ashterot Karnayim, Zuziyawa a Ham, Emawa a Shabe Kiriyatayim,
6 and the Horites on their mount Seir, to El-Paran, which is by the wilderness.
da Horiyawa a ƙasar tudun Seyir har zuwa El Faran kusa da hamada.
7 And they returned, and came to En-mishpat, which is Kadesh, and smote all the country of the Amalekites, and also the Amorites that dwelt at Hazazon-Tamar.
Sa’an nan suka juya suka tafi En Mishfat (wato, Kadesh), suka cinye dukan ƙasar Amalekawa, da kuma Amoriyawa waɗanda suke zaune a Hazazon Tamar.
8 And the king of Sodom and the king of Gomorrah, and the king of Admah, and the king of Zeboim, and the king of Bela, which is Zoar, went out, and they joined battle with them in the vale of Siddim,
Sai sarkin Sodom, sarkin Gomorra, sarkin Adma, sarkin Zeboyim da sarkin Bela (wato, Zowar), suka fita suka ja dāgā a Kwarin Siddim
9 with Chedorlaomer the king of Elam, and Tidal the king of nations, and Amraphel the king of Shinar, and Arioch the king of Ellasar — four kings with the five.
gāba da Kedorlayomer sarkin Elam, Tidal sarkin Goyim, Amrafel sarkin Shinar da Ariyok sarkin Ellasar; sarakuna huɗu gāba da biyar.
10 And the vale of Siddim was full of pits of asphalt. And the kings of Sodom and Gomorrah fled, and fell there: and they that remained fled to the mountain.
Kwarin Siddim kuwa ya cika da ramummukan kwalta, sa’ad da sarakunan Sodom da Gomorra suka gudu kuwa, waɗansu mutane suka fāɗa cikin ramummukan kwaltan, sauran kuwa suka gudu zuwa tuddai.
11 And they took all the property of Sodom and Gomorrah, and all their victuals, and departed.
Sarakunan nan huɗu suka washe dukan kayayyakin Sodom da Gomorra, da kuma dukan abincinsu, sa’an nan suka tafi.
12 And they took Lot and his property, Abram's brother's son, and departed. For he dwelt in Sodom.
Suka kuma kama Lot ɗan ɗan’uwan Abram, wanda yake zaune a Sodom, da kayayyakinsa, suka yi tafiyarsu.
13 And one who had escaped came and told Abram the Hebrew. And he dwelt by the oaks of Mamre the Amorite, the brother of Eshcol, and the brother of Aner. And these were Abram's allies.
Sai wani wanda ya tsira, ya zo ya faɗa wa Abram mutumin Ibraniyawa. Abram kuwa yana zama kusa da manyan itatuwan Mamre, Mamre mutumin Amoriyawa ne ɗan’uwan Eshkol da Aner, su kuwa abokan Abram ne.
14 And Abram heard that his brother was taken captive; and he led out his trained [servants], born in his house, three hundred and eighteen, and pursued [them] as far as Dan.
Da Abram ya ji cewa an kama danginsa, sai ya tara horarrun mutane 318, da aka haifa a gidansa, ya bi sawun sarakunan da suka tafi da Lot, har Dan.
15 And he divided himself against them by night, he and his servants, and smote them, and pursued them as far as Hobah, which is to the left of Damascus.
Da dad dare, Abram ya rarraba mutanensa don su fāɗa wa sarakunan nan, ya ɗibge su, ya kore su har zuwa Hoba, arewa da Damaskus.
16 And he brought back all the property, and brought again his brother Lot and his property, and the women also, and the people.
Ya washe su da kuma dukan kayayyakinsu, ya kuma dawo da Lot danginsa da mallakarsa, tare da mata da sauran mutane.
17 And the king of Sodom went out to meet him after he had returned from smiting Chedorlaomer, and the kings that were with him, into the valley of Shaveh, which is the king's valley.
Bayan Abram ya dawo daga cin Kedorlayomer da sarakunan da suka haɗa kai da shi a yaƙi, sai sarkin Sodom ya fito don yă tarye Abram a Kwarin Shabe (wato, Kwarin Sarki).
18 And Melchisedec king of Salem brought out bread and wine. And he was priest of the Most High God.
Sai Melkizedek sarkin Salem ya kawo burodi da ruwan inabi. Shi firist ne na Allah Mafi Ɗaukaka,
19 And he blessed him, and said, Blessed be Abram of the Most High God, possessor of heavens and earth.
ya albarkaci Abram yana cewa, “Allah Mafi Ɗaukaka Mahaliccin sama da ƙasa yă albarkace Abram.
20 And blessed be the Most High God, who has delivered thine enemies into thy hand. And he gave him the tenth of all.
Kuma albarka ta tabbata ga Allah Mafi Ɗaukaka wanda ya ba da maƙiyanka a hannunka.” Sa’an nan Abram ya ba shi kashi ɗaya bisa goma na kome.
21 And the king of Sodom said to Abram, Give me the souls, and take the property for thyself.
Sarkin Sodom ya ce wa Abram, “Ka ba ni mutanena da ka ƙwace daga hannun sarakunan nan kawai, ka riƙe kayayyakin don kanka.”
22 And Abram said to the king of Sodom, I have lifted up my hand to Jehovah, the Most High God, possessor of heavens and earth,
Amma Abram ya ce, wa sarkin Sodom, “Na ɗaga hannu ga Ubangiji Allah Mafi Ɗaukaka, Mahaliccin sama da ƙasa, na riga na rantse
23 if from a thread even to a sandal-thong, yes, if of all that is thine, I take [anything]...; that thou mayest not say, I have made Abram rich;
cewa ba zan karɓi kome da yake naka ba, ko zare ko maɗaurin takalma, don kada ka ce, ‘Na azurta Abram.’
24 save only that which the young men have eaten, and the portion of the men that went with me, Aner, Eshcol, and Mamre, let them take their portion.
Ba zan karɓi kome ba, sai dai abin da mutanena suka ci da kuma rabon mutanen da suka tafi tare da ni, ga Aner, Eshkol, da Mamre. Bari su ɗauki rabonsu.”

< Genesis 14 >