< Ezekiel 30 >
1 And the word of Jehovah came unto me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Son of man, prophesy and say, Thus saith the Lord Jehovah: Howl ye, Alas for the day!
“Ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Yi kuka kana cewa, “Kaito saboda wannan rana!”
3 For the day is at hand, yea, the day of Jehovah is at hand, a day of clouds; it shall be the time of the nations.
Gama ranar ta yi kusa, ranar Ubangiji ta gabato, ranar gizagizai, lokacin hallaka wa al’ummai.
4 And the sword shall come upon Egypt, and there shall be anguish in Ethiopia, when the slain shall fall in Egypt, and they shall take away her multitude, and her foundations shall be overthrown.
Takobi zai zo a kan Masar, azaba za tă zo a kan Kush. Sa’ad da kisassu za su fāɗi a Masar, za a kwashe dukiyarta a tafi a rushe harsashinta.
5 Cush, and Phut, and Lud, and all the mingled people, and Chub, and the children of the land that is in league, shall fall with them by the sword.
Kush da Fut, Lidiya da dukan Arabiya, Libiya da kuma mutanen ƙasar alkawari za su mutu ta wurin takobi tare da Masar.
6 Thus saith Jehovah: They also that uphold Egypt shall fall; and the pride of her strength shall come down: from Migdol to Syene shall they fall in her by the sword, saith the Lord Jehovah.
“‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Waɗanda suke goyon bayan Masar za su fāɗi ƙarfinta da take fariya da shi zai ƙare. Daga Migdol zuwa Aswan za su mutu ta wurin takobi a cikinta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
7 And they shall be desolated in the midst of the countries that are desolated, and her cities shall be in the midst of the cities that are wasted.
Za su zama kango a cikin ƙasashen da suke kango, biranensu kuwa za su zama kufai a cikin biranen da suka lalace.
8 And they shall know that I [am] Jehovah, when I have set a fire in Egypt, and all her helpers shall be broken.
Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da suka ga na sa wuta wa Masar aka kuma ragargaza masu taimakonta.
9 In that day shall messengers go forth from me in ships, to make careless Ethiopia afraid; and anguish shall come upon them, as in the day of Egypt: for behold, it cometh!
“‘A wannan rana manzanni za su fito daga wurina a jiragen ruwa don su tsorata Kush daga sake jikinta. Azaba za tă kama su a ranar hallakar Masar, gama tabbatacce za tă zo.
10 Thus saith the Lord Jehovah: I will also make the multitude of Egypt to cease by the hand of Nebuchadrezzar king of Babylon.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan kawo ƙarshen mutanen Masar ta hannun Nebukadnezzar sarkin Babilon.
11 He and his people with him, the terrible of the nations, shall be brought to destroy the land; and they shall draw their swords against Egypt, and fill the land with slain.
Shi da sojojinsa, mafi bantsoro cikin al’ummai, za a kawo don su hallaka ƙasar. Za su zāre takuba a kan Masar su kuma cika ƙasar da kisassu.
12 And I will make the rivers dry, and sell the land into the hand of the wicked; and I will make the land desolate, and all that is therein, by the hand of strangers: I Jehovah have spoken [it].
Zan kafe rafuffukan Nilu in sayar da ƙasar ga mugayen mutane; ta hannun baƙi zan sa ƙasar ta lalace da kome da yake cikinta. Ni Ubangiji na faɗa.
13 Thus saith the Lord Jehovah: I will also destroy the idols, and I will cause the images to cease out of Noph; and there shall be no more a prince out of the land of Egypt; and I will put fear in the land of Egypt.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Zan hallaka gumaka in kuma kawo ƙarshen siffofi a Memfis. Ba za a ƙara samun yerima a ƙasar Masar ba, zan kuma baza tsoro a duk fāɗin ƙasar.
14 And I will make Pathros desolate, and will set a fire in Zoan, and will execute judgment in No.
Zan lalace Masar ta Bisa in ƙuna wuta wa Zowan in zartar da hukunci a kan Tebes.
15 And I will pour my fury upon Sin, the stronghold of Egypt; and I will cut off the multitude of No.
Zan kwarara hasalata a kan Felusiyum, kagarar Masar, in kuma datse mutanen Tebes.
16 And I will set a fire in Egypt: Sin shall be in great anguish, and No shall be rent asunder, and at Noph [there shall be] enemies in open day.
Zan ƙuna wuta wa Masar; Felusiyum za tă sha azaba mai zafi. Za a tayar wa Tebes da hankali; Memfis za tă riƙa kasance cikin ɓacin rai.
17 The young men of Aven and of Pibeseth shall fall by the sword; and these shall go into captivity.
Samarin Heliyofolis da Bubastis za su mutu ta wurin takobi, biranen kansu za su tafi bauta.
18 And at Tehaphnehes the day shall be darkened, when I break there the yokes of Egypt, and the pride of her strength shall cease in her; as for her, a cloud shall cover her, and her daughters shall go into captivity.
Duhu ne zai zama rana a Tafanes sa’ad da na karye ikon Masar; a can ƙarfin da take fariya zai ƙare. Za a rufe ta da gizagizai ƙauyukanta kuma za su tafi bauta.
19 Thus will I execute judgments in Egypt; and they shall know that I [am] Jehovah.
Ta haka zan zartar da hukunci a kan Masar, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
20 And it came to pass in the eleventh year, in the first [month], on the seventh of the month, the word of Jehovah came unto me, saying,
A shekara ta goma sha ɗaya, a wata na fari a rana ta goma sha bakwai, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
21 Son of man, I have broken the arm of Pharaoh king of Egypt; and behold, it shall not be bound up to apply remedies, to put a bandage to bind it, to make it strong to hold the sword.
“Ɗan mutum, na karye hannun Fir’auna sarkin Masar. Ba a daure shi don warkarwa ba ko a sa tsinke saboda kada yă zama da ƙarfi har ya riƙe takobi.
22 Therefore thus saith the Lord Jehovah: Behold, I am against Pharaoh king of Egypt, and will break his arms, the strong one, and that which was broken; and I will cause the sword to fall out of his hand.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da Fir’auna sarkin Masar. Zan karye hannuwansa biyu, hannun da yake da kyau da kuma wanda an riga an karya, in kuma sa takobi ya fāɗi daga hannunsa.
23 And I will scatter the Egyptians among the nations, and will disperse them through the countries.
Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
24 And I will strengthen the arms of the king of Babylon, and put my sword in his hand; and I will break Pharaoh's arms, so that he shall groan before him with the groanings of a deadly-wounded [man].
Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon in kuma sa takobina a hannunsa, amma zan karya hannuwan Fir’auna, zai kuwa yi nishi a gabansa kamar mutumin da aka yi wa raunin mutuwa.
25 And I will strengthen the arms of the king of Babylon, and the arms of Pharaoh shall fall down; and they shall know that I [am] Jehovah, when I have put my sword into the hand of the king of Babylon, and he shall have stretched it out upon the land of Egypt.
Zan ƙarfafa hannuwan sarkin Babilon, amma hannuwan Fir’auna za su shanye. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na sa takobi a hannun sarkin Babilon na kuma miƙa shi a kan Masar.
26 And I will scatter the Egyptians among the nations, and disperse them through the countries: and they shall know that I [am] Jehovah.
Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”