< Exodus 19 >
1 In the third month after the departure of the children of Israel out of the land of Egypt, the same day came they [into] the wilderness of Sinai:
A rana ta farko a cikin watan uku bayan da Isra’ilawa suka bar Masar, a wannan rana, suka iso Hamadar Sinai.
2 they departed from Rephidim, and came [into] the wilderness of Sinai, and encamped in the wilderness; and Israel encamped there before the mountain.
Bayan da suka tashi daga Refidim, suka shiga Hamadar Sinai, sai Isra’ilawa suka yi sansani a gaban dutsen.
3 And Moses went up to God, and Jehovah called to him out of the mountain, saying, Thus shalt thou say to the house of Jacob, and tell the children of Israel:
Sai Musa ya hau kan dutsen don yă sadu da Allah, Ubangiji kuwa ya kira shi daga dutsen ya ce, “Wannan shi ne abin da za ka faɗa wa gidan Yaƙub, da kuma abin da za ka faɗa wa mutanen Isra’ila.
4 Ye have seen what I have done to the Egyptians, and [how] I have borne you on eagles' wings and brought you to myself.
‘Ku da kanku kun ga abin da na yi wa Masar, da yadda na ɗauko ku a kan fikafikan gaggafa na kawo ku wurina.
5 And now, if ye will hearken to my voice indeed and keep my covenant, then shall ye be my own possession out of all the peoples — for all the earth is mine —
Yanzu, in kuka yi mini cikakken biyayya, kuka kuma kiyaye yarjejjeniyata, to, za ku zama keɓeɓɓiyar taska a gare ni a cikin dukan al’ummai. Ko da yake duk duniya tawa ce,
6 and ye shall be to me a kingdom of priests, and a holy nation. These are the words which thou shalt speak to the children of Israel.
za ku zama firistoci masu tsarki da kuma al’umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne kalmomin da za ka faɗa wa Isra’ilawa.”
7 And Moses came and called the elders of the people, and laid before them all these words which Jehovah had commanded him.
Sai Musa ya koma ya aika a kira dukan dattawan mutane, ya bayyana dukan kalmomin da Ubangiji ya umarta, ya faɗa.
8 And all the people answered together, and said, All that Jehovah has spoken will we do! And Moses brought the words of the people back to Jehovah.
Dukan mutane suka amsa gaba ɗaya suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa.” Sai Musa ya mayar wa Ubangiji amsar da mutane suka bayar.
9 And Jehovah said to Moses, Lo, I will come to thee in the cloud's thick darkness, that the people may hear when I speak with thee, and believe thee also for ever. And Moses told the words of the people to Jehovah.
Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ina zuwa wurinka a cikin baƙin hadari, domin mutane su ji ni ina maganar da kai, domin su amince da kai koyaushe.” Sa’an nan Musa ya faɗa wa Ubangiji abin da mutane suka ce.
10 And Jehovah said to Moses, Go to the people, and hallow them to-day and to-morrow, and let them wash their clothes;
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin mutanen, ka tsarkake su yau da gobe, ka sa su wanke tufafinsu.
11 and let them be ready for the third day; for on the third day Jehovah will come down before the eyes of all the people on mount Sinai.
Su zama da shiri a rana ta uku, gama a ranar ce Ubangiji zai sauko a kan Dutsen Sinai a idon dukan mutane.
12 And set bounds round about the people, saying, Take heed to yourselves, [not] to go up unto the mountain nor touch the border of it: whatever toucheth the mountain shall certainly be put to death:
Sai ka yi wa jama’a iyaka kewaye da dutsen, ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ku mai da hankali, kada ku hau dutsen ko ku taɓa gefensa. Duk wanda ya taɓa dutsen, lalle za a kashe shi.
13 not a hand shall touch it, but it shall certainly be stoned, or shot through; whether it be a beast or a man, it shall not live. When the long drawn note of the trumpet soundeth, they shall come up to the mountain.
Za a jajjefe shi da duwatsu, ko a harbe shi da kibiyoyi, ba hannun da zai taɓa shi. Mutum ko dabbar da ya taɓa, ba za a bar shi da rai ba.’ Lokacin da aka ji muryar ƙaho ne kawai za su iya taru a gindin dutsen.”
14 And Moses came down from the mountain to the people, and hallowed the people; and they washed their clothes.
Bayan da Musa ya gangara wurin mutane, ya tsarkake su, sai suka wanke tufafinsu.
15 And he said to the people, Be ready for the third day; do not come near [your] wives.
Sa’an nan ya ce wa mutane, “Ku shirya kanku domin rana ta uku. Ku ƙame kanku daga yin jima’i.”
16 And it came to pass on the third day, when it was morning, that there were thunders and lightnings and a heavy cloud on the mountain, and the sound of the trumpet exceeding loud; and the whole people that was in the camp trembled.
A safiyar rana ta uku, aka yi tsawa, da walƙiyoyi, sai ga girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama’ar da suke cikin sansani suka yi rawar jiki.
17 And Moses brought the people out of the camp to meet with God; and they stood at the foot of the mountain.
Sa’an nan Musa ya jagoranci mutane daga sansani domin su sadu da Allah, sai suka tsaya a gefen dutsen.
18 And the whole of mount Sinai smoked, because Jehovah descended on it in fire; and its smoke ascended as the smoke of a furnace; and the whole mountain shook greatly.
Dutsen Sinai kuwa ya tunnuƙe duka da hayaƙi, gama Ubangiji ya sauko a bisan dutsen cikin wuta. Hayaƙin ya hau kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya, duk dutsen ya yi rawa da ƙarfi,
19 And the sound of the trumpet increased and became exceeding loud; Moses spoke, and God answered him by a voice.
sai karar ƙaho ya yi ta ƙaruwa. Sa’an nan Musa ya yi magana, murya Allah kuwa ta amsa masa.
20 And Jehovah came down on mount Sinai, on the top of the mountain; and Jehovah called Moses to the top of the mountain, and Moses went up.
Ubangiji ya sauko a kan ƙwanƙolin Dutsen Sinai, ya kira Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen. Musa kuwa ya haura
21 And Jehovah said to Moses, Go down, testify to the people that they break not through to Jehovah to gaze, and many of them perish.
sai Ubangiji ya ce masa, “Ka sauka ka faɗa wa jama’a, kada su kuskura su ƙetare layin iyakan nan, garin son zuwa don ganin Ubangiji, gama duk waɗanda suka yi haka za su mutu.
22 And the priests also, who come near to Jehovah, shall hallow themselves, lest Jehovah break forth on them.
Ko firistocin da za su kusato Ubangiji sai su tsarkake kansu, don kada in hallaka su.”
23 And Moses said to Jehovah, The people cannot come up to mount Sinai; for thou hast testified to us, saying, Set bounds about the mountain, and hallow it.
Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su hau Dutsen Sinai ba, gama kai da kanka ka gargaɗe mu, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen ku kuma tsarkake shi.’”
24 And Jehovah said to him, Go, descend, and thou shalt come up, thou, and Aaron with thee; but the priests and the people shall not break through to go up to Jehovah, lest he break forth on them.
Ubangiji ya amsa, “Sauka ka kawo Haruna tare da kai. Amma kada firistoci da mutane su zarce iyakan nan, a kan za su zo wurin Ubangiji, don kada in hallaka su.”
25 So Moses went down to the people, and told them.
Saboda haka Musa ya sauka wurin mutane ya kuma faɗa musu.