< Deuteronomy 6 >

1 And these are the commandments, the statutes, and the ordinances, which Jehovah your God commanded to teach you, that ye may do them in the land whereunto ye pass over to possess it,
Waɗannan su ne umarnai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnku ya umarce ni in koya muku don ku kiyaye a ƙasar da kuke haye Urdun don mallaka,
2 that thou mayest fear Jehovah thy God, to keep all his statutes and his commandments which I command thee, thou, and thy son, and thy son's son, all the days of thy life; and that thy days may be prolonged.
saboda ku,’ya’yanku, da kuma’ya’yansu bayansu za su ji tsoron Ubangiji Allahnku muddin kuna rayuwa ta wurin kiyaye dukan ƙa’idodinsa da umarnan da na ba ku, da kuma don ku yi tsawon rai.
3 And thou shalt hear, Israel, and take heed to do [them]; that it may be well with thee, and that ye may increase greatly, as Jehovah the God of thy fathers hath said unto thee, in a land flowing with milk and honey.
Ku ji, ya Isra’ila, ku kuma kula, ku kiyaye su don yă zama muku da lafiya, ku kuma ƙaru sosai a ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji, Allahn kakanninku ya yi muku alkawari.
4 Hear, Israel: Jehovah our God is one Jehovah;
Ku ji, ya Isra’ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne.
5 and thou shalt love Jehovah thy God with all thy heart, and with all thy soul, and with all thy strength.
Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da dukan zuciyarku, da dukan ranku, da kuma dukan ƙarfinku.
6 And these words, which I command thee this day, shall be in thy heart;
Waɗannan umarnai da nake ba ku a yau, za su kasance a zukatanku.
7 and thou shalt impress them on thy sons, and shalt talk of them when thou sittest in thy house, and when thou goest on the way, and when thou liest down, and when thou risest up.
Ku koya wa’ya’yanku su da himma. Yi musu magana game da su sa’ad da kuke zaune a gida, da sa’ad da kuke tafiya a hanya, sa’ad da kuke kwance, da sa’ad da kuka tashi.
8 And thou shalt bind them for a sign on thy hand, and they shall be for frontlets between thine eyes.
Ku ɗaura su su zama alamu a hannuwanku, ku kuma ɗaura su a goshinku.
9 And thou shalt write them upon the posts of thy house, and upon thy gates.
Ku rubuta su a dogaran ƙofofin gidajenku, da ƙofofinku.
10 And it shall be, when Jehovah thy God bringeth thee into the land which he swore unto thy fathers, to Abraham, to Isaac, and to Jacob, to give thee: great and good cities which thou buildedst not,
Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku cikin ƙasar da ya rantse ga kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, yă ba ku, ƙasa mai girma, mai manyan biranen da ba ku kuka gina ba,
11 and houses full of everything good which thou filledst not, and wells digged which thou diggedst not, vineyards and oliveyards which thou plantedst not, and thou shalt have eaten and shalt be full;
gidaje cike da kowane irin abubuwa masu kyau, da ba ku kuka tanadar ba, rijiyoyin da ba ku kuka haƙa ba, da gonakin inabi da itatuwan zaitun da ba ku kuka shuka ba, sa’ad da kuwa kuka ci, kuka kuma ƙoshi,
12 [then] beware lest thou forget Jehovah who brought thee forth out of the land of Egypt, out of the house of bondage.
ku yi hankali cewa ba ku manta da Ubangiji wanda ya fitar da ku daga Masar, da gidan bauta ba.
13 Thou shalt fear Jehovah thy God, and serve him, and shalt swear by his name.
Ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa shi kaɗai, ku kuma yi alkawaranku da sunansa.
14 Ye shall not go after other gods, of the gods of the peoples that are round about you;
Kada ku bi waɗansu alloli, allolin mutanen da suke kewaye da ku;
15 for Jehovah thy God is a jealous God in thy midst; lest the anger of Jehovah thy God be kindled against thee, and he destroy thee from the face of the earth.
gama Ubangiji Allahnku, wanda yake cikinku, Allah ne mai kishi, fushinsa kuma zai yi ƙuna gāba da ku, zai kuma hallaka ku daga fuskar ƙasar.
16 Ye shall not tempt Jehovah your God, as ye tempted him in Massah.
Kada ku gwada Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi a Massa.
17 Ye shall diligently keep the commandments of Jehovah your God, and his testimonies, and his statutes, which he hath commanded thee.
Ku tabbata kun kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, da farillansa da kuma ƙa’idodinsa da ya ba ku.
18 And thou shalt do what is right and good in the sight of Jehovah, that it may be well with thee, and that thou mayest enter in and possess the good land which Jehovah swore unto thy fathers,
Ku aikata abin da yake daidai da kuma mai kyau a idon Ubangiji, don yă zama muka da lafiya, ku kuwa shiga ku mallaki ƙasa mai kyau da Ubangiji ya yi alkawari da rantsuwa ga kakanninku.
19 thrusting out all thine enemies from before thee, as Jehovah hath spoken.
Zai kuwa korin dukan abokan gābanku da suke gabanku, yadda Ubangiji ya faɗa.
20 When thy son shall ask thee in time to come, saying, What are the testimonies, and the statutes, and the ordinances, which Jehovah our God hath commanded you?
Nan gaba, sa’ad da’ya’yanku suka tambaye ku, “Mene ne ma’anar farillai, ƙa’idodi da kuma dokokin da Ubangiji Allahnmu ya umarce ku?”
21 then thou shalt say unto thy son, We were Pharaoh's bondmen in Egypt; and Jehovah brought us out of Egypt with a powerful hand;
Sai ku gaya musu, “Dā mu bayin Fir’auna ne a Masar, amma Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu masu ƙarfi.
22 and Jehovah shewed signs and wonders, great and grievous, upon Egypt, upon Pharaoh, and upon all his household, before our eyes;
A idanunmu Ubangiji ya aikata manyan alamu masu banmamaki, da al’ajabai gāba da Masarawa, da Fir’auna, da kuma dukan gidansa.
23 and he brought us out thence, that he might bring us in, to give us the land which he swore unto our fathers.
Amma ya fitar da mu daga can domin yă kawo mu cikin ƙasar da ya yi wa kakanninmu alkawari tare da rantsuwa zai ba mu.
24 And Jehovah commanded us to do all these statutes, to fear Jehovah our God, for our good continually, that he might preserve us alive, as it is this day.
Ubangiji ya umarce mu mu yi biyayya da dukan waɗannan ƙa’idodi, mu kuma ji tsoron Ubangiji Allahnmu, saboda kullum mu ci gaba, a kuma bar mu da rai, kamar yadda yake a yau.
25 And it shall be our righteousness if we take heed to do all these commandments before Jehovah our God, as he hath commanded us.
In kuma muka kula, muka kiyaye dukan dokokin nan a gaban Ubangiji Allahnmu, kamar yadda ya umarce mu, wannan zai zama adalci a gare mu.”

< Deuteronomy 6 >