< Deuteronomy 32 >
1 Give ear, ye heavens, and I will speak; And hear, O earth, the words of my mouth!
Ku saurara, ya ku sammai, zan yi magana; bari duniya ta ji maganar bakina.
2 My doctrine shall drop as rain, My speech flow down as dew, As small rain upon the tender herb, And as showers on the grass.
Bari koyarwata tă zubo kamar ruwan sama kalmomina kuma su sauko kamar raɓa, kamar yayyafi a kan sabuwar ciyawa, kamar ruwan sama mai yawa a kan tsirai marasa ƙarfi.
3 For the name of Jehovah will I proclaim: Ascribe greatness unto our God!
Zan yi shelar sunan Ubangiji. Ku yabi girman Allahnmu!
4 [He is] the Rock, his work is perfect, For all his ways are righteousness; A God of faithfulness without deceit, Just and right is he.
Shi Dutse ne, ayyukansa cikakku ne, dukan hanyoyinsa kuwa masu adalci ne. Allah mai aminci, wanda ba ya yin rashi gaskiya, shi mai adalci ne, nagari ne kuma.
5 They have dealt corruptly with him; Not his children's is their spot: — A crooked and perverted generation!
Sun aikata mugunta a gabansa; saboda abin kunyarsu, su ba’ya’yansa ba ne, amma wata muguwar tsara ce, karkatacciya.
6 Do ye thus requite Jehovah, Foolish and unwise people? Is not he thy father that hath bought thee? Hath he not made thee and established thee?
Haka za ku biya Ubangiji, Ya ku wawaye da kuma mutane marasa hikima? Shi ba Ubanku ba ne, Mahaliccinku, wanda ya yi ku, ya kuma siffanta ku?
7 Remember the days of old, Consider the years of generation to generation; Ask thy father, and he will shew thee; Thine elders, and they will tell thee.
Ku tuna da kwanakin dā, ku tuna da tsararrakin da suka wuce tun tuni, Ku tambayi iyayenku, za su faɗa muku, dattawanku, za su kuma bayyana muku.
8 When the Most High assigned to the nations their inheritance, When he separated the sons of Adam, He set the bounds of the peoples According to the number of the children of Israel.
Sa’ad da Mafi Ɗaukaka ya ba da al’ummai gādonsu, sa’ad da ya raba dukan’yan adam, ya kafa iyakoki wa mutane bisa ga yawan’ya’yan Isra’ila maza.
9 For Jehovah's portion is his people; Jacob the lot of his inheritance.
Gama rabon Ubangiji shi ne mutanensa, Yaƙub shi ne rabon gādonsa.
10 He found him in a desert land, And in the waste, howling wilderness; He compassed him about, he watched over him, He preserved him as the apple of his eye.
A cikin hamada ya same shi, a jeji marar amfani, inda namomi suke kuka. Ya tsare shi, ya kuma lura da shi; ya bi da shi kamar ƙwayar idonsa,
11 As the eagle stirreth up its nest, Hovereth over its young, Spreadeth out its wings, Taketh them, beareth them on its feathers,
kamar gaggafar da take yawo a kan sheƙarta tana rufe’ya’yanta, ta buɗe fikafikanta don tă kwashe su tă ɗauke su a kafaɗunta.
12 So Jehovah alone did lead him, And no strange god [was] with him.
Ubangiji kaɗai ya jagorance shi; babu wani baƙon gunkin da yake tare da shi.
13 He made him ride on the high places of the earth, And he ate the produce of the field; And he made him suck honey out of the crag, And oil out of the flinty rock;
Ya sa shi ya hau ƙwanƙolin dutse ya ciyar da shi da amfanin gona. Ya shayar da shi da zuma daga dutse, da kuma mai daga dutsen ƙanƙara,
14 Cream of kine, and milk of sheep, With the fat of lambs, And rams of the breed of Bashan, and he-goats, With the fat of kidneys of wheat; And thou didst drink pure wine, the blood of the grape.
da kindirmo da madara daga shanu da tumaki da ƙibabbun tumaki da awaki, da zaɓaɓɓun ragunan Bashan da kuma ƙwayoyin alkama mafi kyau. Ka sha ruwan inabi ja wur mai kumfa.
15 Then Jeshurun grew fat, and kicked — Thou art waxen fat, Thou art grown thick, And thou art covered with fatness; — He gave up God who made him, And lightly esteemed the Rock of his salvation.
Yeshurun ya yi ƙiba, ya yi kauri; cike da abinci, ya zama da nauyi, ya kuma zama sumul. Ya yashe Allahn da ya yi shi, ya ƙi Dutse Cetonsa.
16 They moved him to jealousy with strange gods, With abominations did they provoke him to anger.
Suka sa shi kishi saboda baƙin allolinsu, suka husata shi da gumakan banƙyamarsu.
17 They sacrificed unto demons who are not God; To gods whom they knew not, To new ones, who came newly up, Whom your fathers revered not.
Suka yi hadaya ga aljanu, waɗanda ba Allah ba, ga allolin da ba su sani ba, ga allolin da aka shigo da su daga baya, allolin da kakanninku ba su ji tsoronsu ba.
18 Of the Rock that begot thee wast thou unmindful, And thou hast forgotten God who brought thee forth.
Kuka rabu da Dutsen da ya zama mahaifi gare ku; kuka manta da Allahn da ya haife ku.
19 And Jehovah saw it, and despised them, Because of the provoking of his sons and of his daughters.
Ubangiji ya ga wannan ya kuma ƙi su, domin’ya’yansa maza da mata sun husata shi.
20 And he said, I will hide my face from them, I will see what their end shall be; For they are a perverse generation, Children in whom is no faithfulness.
Ya ce, “Zan ɓoye fuskata daga gare su, in ga ƙarshensu; gama su muguwar tsara ce,’ya’ya ne marasa aminci.
21 They have moved me to jealousy with that which is no God; They have exasperated me with their vanities; And I will move them to jealousy with that which is not a people; With a foolish nation will I provoke them to anger.
Sun sa ni kishi ta wurin abin da ba allah ba, suka kuma husata ni da gumakansu na wofi. Zan sa su yi kishi ta wurin waɗanda ba mutane ba; zan sa su yi fushi ta wurin al’ummar da ba ta da sani.
22 For a fire is kindled in mine anger, And it shall burn into the lowest Sheol, And shall consume the earth and its produce, And set fire to the foundations of the mountains. (Sheol )
Gama fushina ya kama wuta, tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za tă cinye duniya da girbinta, tă kuma sa wuta a tussan duwatsu. (Sheol )
23 I will heap mischiefs upon them; Mine arrows will I spend against them.
“Zan tula masifu a kansu in kuma gama kibiyoyina a kansu.
24 They shall be consumed with hunger, and devoured with burning heat, And with poisonous pestilence; And the teeth of beasts will I send against them, With the poison of what crawleth in the dust.
Zan aika da yunwa mai tsanani a kansu, zazzaɓi mai zafi da muguwar annoba; zan aika da haƙoran namun jeji a kansu, da dafin mesa masu ja da ciki.
25 From without shall the sword bereave them, and in the chambers, terror — Both the young man and the virgin, The suckling with the man of gray hairs.
Waɗanda suke a waje, takobi zai kashe su, a cikin gidajensu kuma tsoro zai mamaye su.’Yan maza da’yan mata za su hallaka, haka ma jarirai da maza masu furfura.
26 I would say, I will scatter, I will make the remembrance of them to cease from among men,
Na ce zan watsar da su in sa a manta da su a tunanin’yan adam.
27 If I did not fear provocation from the enemy, Lest their adversaries should misunderstand it, Lest they should say, Our hand is high, and Jehovah has not done all this.
Amma ina tsoron tsokanar abokin gāba, don kada abokan gāba su kāsa ganewa har su ce, ‘Hannunmu ne ya yi nasara; ba Ubangiji ne ya aikata dukan wannan ba.’”
28 For they are a nation void of counsel, And understanding is not in them.
Al’ummai ne marasa azanci, babu ganewa a cikinsu.
29 Oh that they had been wise! they would have understood this, They would have considered their latter end!
A ce su masu hikima ne har su gane wannan su gane abin da ƙarshensu zai zama!
30 How could one chase a thousand, And two put ten thousand to flight, Were it not that their Rock had sold them, And Jehovah had delivered them up?
Yaya mutum guda zai kore dubu, mutum biyu su sa dubu goma su gudu, sai ko Dutsensu ya sayar da su, sai ko Ubangiji ya bashe su.
31 For their rock is not as our Rock: Let our enemies themselves be judges.
Gama dutsensu ba kamar Dutsenmu ba ne, abokan gābanmu sun san da haka.
32 For their vine is of the vine of Sodom, And of the fields of Gomorrah: Their grapes are grapes of poison, Bitter are their clusters;
Kuringarsu ta fito daga kuringar Sodom ne, daga gonakin Gomorra kuma.’Ya’yan inabinsu dafi ne, nonnansu masu ɗaci ne.
33 Their wine is the poison of dragons, And the cruel venom of vipers.
Ruwan inabinsu dafin macizai ne, mugun dafin gamshaƙa ne.
34 Is not this hidden with me, Sealed up among my treasures?
“Ban jibge wannan a ma’ajiya na kuma yimƙe shi a taskokina ba?
35 Vengeance is mine, and recompense, For the time when their foot shall slip. For the day of their calamity is at hand, And the things that shall come upon them make haste.
Sakayya nawa ne, zan kuwa ɗau fansa. A cikin lokaci, ƙafarsu za tă yi santsi; ranar masifarsu ta yi kusa hallakarsu kuma tana gaggautawa a kansu.”
36 For Jehovah will judge his people, And shall repent in favour of his servants; When he seeth that power is gone, And there is none shut up or left.
Ubangiji zai shari’anta mutanensa yă kuma ji tausayin bayinsa sa’ad da ya ga ƙarfinsu ya ƙare babu kowa kuma da ya rage, bawa ko’yantacce.
37 And he shall say, Where are their gods, Their rock in whom they trusted,
Zai ce, “To, ina allolinsu, dutsen da suka yi mafaka a ciki,
38 Who ate the fat of their sacrifices, [And] drank the wine of their drink-offering? Let them rise up and help you, That there may be a protection over you.
allolin da suka ci kitsen hadayunsu suka kuma sha ruwan inabin hadayunsu? Ku sa su tashi su taimake ku mana! Bari su ba ku mafaka!
39 See now that I, I am HE, And there is no god with me; I kill, and I make alive; I wound, and I heal, And there is none that delivereth out of my hand,
“Ku duba yanzu cewa ni ne Shi! Ba wani allah in ban da ni. Nakan kashe in kuma rayar, nakan sa rauni in kuma warkar, ba wanda yake da iko yă cece wani daga hannuna.
40 For I lift up my hand to the heavens, and say, I live for ever!
Na ɗaga hannu sama na kuma furta. Muddin ina raye har abada,
41 If I have sharpened my gleaming sword, And my hand take hold of judgment, I will render vengeance to mine adversaries, And will recompense them that hate me.
sa’ad da na wasa takobi mai walƙiya hannuna kuwa ya cafke shi don yin hukunci, zan ɗau fansa a kan abokan gābana in sāka wa waɗanda suke ƙina.
42 Mine arrows will I make drunk with blood, And my sword shall devour flesh; [I will make them drunk] with the blood of the slain and of the captives, With the head of the princes of the enemy.
Zan sa kibiyoyina su bugu da jini, yayinda takobina yana cin nama, jinin kisassu da na kamammu, kawunan shugabannin abokan gāba.”
43 Shout for joy, ye nations, with his people, For he avengeth the blood of his servants, And rendereth vengeance to his enemies, And maketh atonement for his land, for his people.
Ku yi farin ciki, ya ku al’ummai, tare da mutanensa, gama zai rama ɗau fansar jinin bayinsa; zai ɗau fansa a kan abokan gābansa yă kuma yi kafara domin ƙasarsa da mutanensa.
44 And Moses came and spoke all the words of this song in the ears of the people, he and Hoshea the son of Nun.
Sai Musa ya zo da Yoshuwa ɗan Nun suka faɗa dukan waɗannan kalmomi wannan waƙa a kunnen mutane.
45 And when Moses had ended speaking all these words to all Israel,
Sa’ad da Musa ya gama karanta waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila,
46 he said unto them, Set your hearts unto all the words that I testify among you this day, which ye shall command your children to take heed to do, all the words of this law.
ya ce musu, “Ku riƙe dukan kalmomin da na furta muku a yau, don ku umarce’ya’yanku su lura, su yi biyayya da dukan kalmomin wannan doka.
47 For it is no vain word for you, but it is your life, and through this word ye shall prolong your days on the land whereunto ye pass over the Jordan to possess it.
Ba kalmomi kurum ba ne dominku, amma har ranku ma. Ta wurinsu za ku yi tsawon rai a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
48 And Jehovah spoke to Moses that same day, saying,
A wannan rana Ubangiji ya ce wa Musa,
49 Go up into this mountain Abarim, mount Nebo, which is in the land of Moab, which is opposite Jericho; and behold the land of Canaan, which I give unto the children of Israel for a possession,
“Ka hau Duwatsun Abarim zuwa Dutsen Nebo a Mowab, tsallake daga Yeriko, ka hangi Kan’ana, ƙasar da nake ba wa Isra’ilawa gādo.
50 and die on the mountain whither thou goest up, and be gathered unto thy peoples, as Aaron thy brother died on mount Hor, and was gathered unto his peoples;
A can kan dutsen da ka hau za ka mutu a kuma tara ka ga mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya mutu a Dutsen Hor aka kuma tara shi ga mutanensa.
51 because ye trespassed against me among the children of Israel at the waters of Meribah-Kadesh, in the wilderness of Zin; because ye hallowed me not in the midst of the children of Israel.
Wannan kuwa domin ku biyu kun fid da aminci gare ni a gaban Isra’ilawa a ruwan Meriba ta Kadesh, a Hamadar Zin kuma saboda ba ku riƙe tsarkina a cikin Isra’ilawa ba.
52 For thou shalt see the land before [thee]; but thou shalt not go thither unto the land which I give the children of Israel.
Saboda haka, za ka ga ƙasar daga nesa kawai; ba za ka shiga ƙasar da nake ba wa mutanen Isra’ila ba.”