< 2 Timothy 2 >

1 Thou therefore, my child, be strong in the grace which [is] in Christ Jesus.
Domin wannan kai, dana, ka karfafa cikin alherin da ke cikin Almasihu Yesu.
2 And the things thou hast heard of me in the presence of many witnesses, these entrust to faithful men, such as shall be competent to instruct others also.
Abubuwan da ka ji daga gare ni a bainar jama'a masu yawa, ka danka su ga mutane masu aminci da za su iya koya wa wadansu kuma.
3 Take thy share in suffering as a good soldier of Jesus Christ.
Ka daure shan tsanani tare da ni, kamar amintaccen sojan Almasihu Yesu.
4 No one going as a soldier entangles himself with the affairs of life, that he may please him who has enlisted him as a soldier.
Ba bu sojan da zai yi bauta yayin da ya nannade kansa da al'amuran wannan rayuwar, domin ya gamshi shugabansa.
5 And if also any one contend [in the games], he is not crowned unless he contend lawfully.
Hakanan, idan wani yana gasa a matsayin dan wasa, ba zai sami rawani ba tukuna har sai in ya karasa tseren bisa ga ka'idodin gasar.
6 The husbandman must labour before partaking of the fruits.
Wajibi ne manomi mai kwazon aiki ya fara karbar amfanin gonarsa.
7 Think of what I say, for the Lord will give thee understanding in all things.
Ka yi tunani game da abin da na ke gaya maka, gama Ubangiji zai ba ka ganewa a cikin komai.
8 Remember Jesus Christ raised from among [the] dead, of [the] seed of David, according to my glad tidings,
Ka tuna da Yesu Almasihu, daga zuriyar Dauda, wanda a ka tayar daga matattu. Bisa ga wa'azin bisharata,
9 in which I suffer even unto bonds as an evil-doer: but the word of God is not bound.
wanda na ke shan wahala har ya kai ga dauri kamar mai laifi. Amma maganar Allah ba a daure ta ba.
10 For this cause I endure all things for the sake of the elect, that they also may obtain the salvation which [is] in Christ Jesus with eternal glory. (aiōnios g166)
Saboda haka na jure wa dukkan abubuwa domin wadanda aka zaba, saboda su ma su sami ceton da ke cikin Almasihu Yesu, da daukaka madawwamiya. (aiōnios g166)
11 The word [is] faithful; for if we have died together with [him], we shall also live together;
Wannan magana tabbatacciya ce: “Idan mun mutu tare da shi, za mu kuma rayu tare da shi.
12 if we endure, we shall also reign together; if we deny, he also will deny us;
Idan mun jure, zamu kuma yi mulki tare da shi. Idan mun yi musun sa, shi ma zai yi musun mu.
13 if we are unfaithful, he abides faithful, for he cannot deny himself.
Idan mun zama marasa aminci, shi mai aminci ne koyaushe, domin shi ba zai yiwu ya musunta kansa ba.”
14 Of these things put in remembrance, testifying earnestly before the Lord not to have disputes of words, profitable for nothing, to the subversion of the hearers.
Ka yi ta tuna masu da wadannan abubuwan. Ka yi masu kashedi a gaban Allah kada su yi ta dauki ba dadi game da kalmomi. Saboda wannan bai da wani amfani. Domin wannan zai halakar da ma su sauraro.
15 Strive diligently to present thyself approved to God, a workman that has not to be ashamed, cutting in a straight line the word of truth.
Ka yi iyakacin kokarika domin ka mika kanka ma'aikacin Allah wanda aka tabbatar, wanda babu dalilin kunya a gareshi. Wanda ya ke koyar da kalmar gaskiya daidai.
16 But profane, vain babblings shun, for they will advance to greater impiety,
Ka guje wa masu maganar sabo, wanda ya kan kara kaiwa ga rashin bin Allah.
17 and their word will spread as a gangrene; of whom is Hymenaeus and Philetus;
Maganarsu za ta yadu kamar ciwon daji. Daga cikinsu akwai Himinayus da Filitus.
18 [men] who as to the truth have gone astray, saying that the resurrection has taken place already; and overthrow the faith of some.
Wadannan mutanen sun kauce wa gaskiya. Sun fadi cewa an rigaya an yi tashin matattu. Suka birkitar da bangaskiyar wadansu.
19 Yet the firm foundation of God stands, having this seal, [The] Lord knows those that are his; and, Let every one who names the name of [the] Lord withdraw from iniquity.
Duk da haka, ginshikin Allah ya tabbata. Ya na da wannan hatimi: “Ubangiji ya san wadanda ke nasa,” Kuma “Duk mai kira bisa ga sunan Ubangiji dole ya rabu da rashin adalci.”
20 But in a great house there are not only gold and silver vessels, but also wooden and earthen; and some to honour, and some to dishonour.
A gida mai wadata, ba kayayyaki na zinariya da azurfa ba ne kawai. Haka kuma akwai kayayyaki na itace da yunbu. Wadansu domin aikin mai daraja, wadansu kuma ga aiki mara daraja.
21 If therefore one shall have purified himself from these, [in separating himself from them], he shall be a vessel to honour, sanctified, serviceable to the Master, prepared for every good work.
Idan wani ya tsarkake kansa daga rashin daraja, shi kayan aiki ne mai daraja. An kebe shi, abin aiki domin mai gidan, kuma a shirye domin kowanne aiki mai kyau.
22 But youthful lusts flee, and pursue righteousness, faith, love, peace, with those that call upon the Lord out of a pure heart.
Ka guje wa sha'awoyi na kuruciya, ka nemi adalci, bangaskiya, kauna da salama da wadanda suke kira ga sunan Ubangiji daga zuciya mai tsabta.
23 But foolish and senseless questionings avoid, knowing that they beget contentions.
Amma ka ki tambayoyi na wauta da jahilci. Ka sani sukan haifar da gardandami.
24 And a bondman of [the] Lord ought not to contend, but be gentle towards all; apt to teach; forbearing;
Tilas bawan Ubangiji ya guje wa jayayya. A maimakon haka dole ya zama mai tawali'u ga kowa, mai iya koyarwa, kuma mai hakuri.
25 in meekness setting right those who oppose, if God perhaps may sometime give them repentance to acknowledgment of [the] truth,
Dole ne ya koyarwa mutane da su ke jayayya da shi a cikin tawali'u. Watakila Allah ya ba su ikon tuba domin sanin gaskiyar.
26 and that they may awake up out of the snare of the devil, [who are] taken by him, for his will.
Suna iya sake dawowa cikin hankalinsu kuma su bar tarkon Ibilis, bayan da ya cafke su domin nufinsa.

< 2 Timothy 2 >