< 2 John 1 >

1 The elder to [the] elect lady and her children, whom I love in truth, and not I only but also all who have known the truth,
Dattijon nan, Zuwa ga uwargida zaɓaɓɓiya da kuma’ya’yanta, waɗanda nake ƙauna ƙwarai da gaske kuma ba ni kaɗai ba, amma har da dukan waɗanda suka san gaskiya.
2 for the truth's sake which abides in us and shall be with us to eternity. (aiōn g165)
Muna ƙaunarku saboda gaskiyan nan, wadda take cikinmu za tă kuma kasance tare da mu har abada. (aiōn g165)
3 Grace shall be with you, mercy, peace from God [the] Father, and from [the] Lord Jesus Christ, the Son of the Father, in truth and love.
Alheri, jinƙai da kuma salama daga Allah Uba da kuma Yesu Kiristi, Ɗan Uba, su kasance tare da mu cikin gaskiya da ƙauna.
4 I rejoiced greatly that I have found of thy children walking in truth, as we have received commandment from the Father.
Na yi farin ciki ƙwarai, da na sami waɗansu’ya’yanki suna tafiya cikin gaskiya, kamar yadda Uba ya umarce mu.
5 And now I beseech thee, lady, not as writing to thee a new commandment, but that which we have had from [the] beginning, that we should love one another.
Yanzu kuma, uwargida ƙaunatacciya, ba sabon umarni nake rubuta miki ba sai dai wanda muke da shi tun farko. Ina roƙo cewa mu ƙaunaci juna.
6 And this is love, that we should walk according to his commandments. This is the commandment, according as ye have heard from the beginning, that ye might walk in it.
Ƙauna, ita ce mu yi biyayya ga umarnansa. Kamar yadda kuka ji tun da fari, umarninsa shi ne ku yi zaman ƙauna.
7 For many deceivers have gone out into the world, they who do not confess Jesus Christ coming in flesh — this is the deceiver and the antichrist.
Masu ruɗi da yawa, waɗanda ba su yarda da zuwan Yesu Kiristi cikin jiki ba, sun riga sun fito a duniya. Duk irin mutumin nan mai ruɗi ne kuma magabcin Kiristi.
8 See to yourselves, that we may not lose what we have wrought, but may receive full wages.
Ku lura don kada ku yi hasarar aikin da kuka yi, sai dai ku sami cikakken lada.
9 Whosoever goes forward and abides not in the doctrine of the Christ has not God. He that abides in the doctrine, he has both the Father and the Son.
Duk mutumin da bai tsaya a kan koyarwar Kiristi ba, amma ya yi ƙari a kanta, mutumin nan ba shi da Allah. Amma wanda ya tsaya a kan koyarwar Kiristi, yana da Uban da kuma Ɗan.
10 If any one come to you and bring not this doctrine, do not receive him into [the] house, and greet him not;
Duk wanda ya zo wurinku bai kuma kawo koyarwan nan ba, kada ku karɓe shi a gidanku ko ku marabce shi.
11 for he who greets him partakes in his wicked works.
Duk wanda ya karɓe shi yana tarayya da mugun aikinsa ke nan.
12 Having many things to write to you, I would not with paper and ink; but hope to come to you, and to speak mouth to mouth, that our joy may be full.
Ina da abubuwa da dama da zan rubuta muku, sai dai ba na so in yi amfani da takarda da inki in rubuta. A maimako, ina fata in ziyarce ku in kuma yi magana da ku fuska da fuska, domin farin cikinmu yă zama cikakke.
13 The children of thine elect sister greet thee.
’Ya’yan’yar’uwarki wadda Allah ya keɓe, suna gaishe ku.

< 2 John 1 >