< 2 Corinthians 1 >
1 Paul, apostle of Jesus Christ by God's will, and the brother Timotheus, to the assembly of God which is in Corinth, with all the saints who are in the whole of Achaia.
Bulus, manzon Almasihu Yesu ta wurin nufin Allah, da kuma Timoti dan'uwan mu, zuwa ga Ikilisiyar Allah da ke a Korantus, da kuma dukan 'yan'uwa da ke yankin kasar Akaya.
2 Grace to you, and peace from God our Father, and [the] Lord Jesus Christ.
Bari alheri ya kasance tare da ku da kuma salama ta Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.
3 Blessed [be] the God and Father of our Lord Jesus Christ, the Father of compassions, and God of all encouragement;
Bari yabo ya tabbata ga Allah da kuma Uba na Ubangijinmu Yesu Almasihu. Shine Uba na dukan jiyejiyenkai, da kuma Allah na dukan ta'aziya.
4 who encourages us in all our tribulation, that we may be able to encourage those who are in any tribulation whatever, through the encouragement with which we ourselves are encouraged of God.
Allah yana ta'azantar da mu a cikin dukan wahalarmu, domin mu iya ta'azantar da wadanda ke cikin kowace wahala. Muna ta'azantar da wasu da irin ta'aziyar da Allah ke ta'azantar da mu.
5 Because, even as the sufferings of the Christ abound towards us, so through the Christ does our encouragement also abound.
Gama kamar yadda wahalhalun Almasihu suka karu domin mu, haka kuma ta'aziyarmu ta yawaita cikin Almasihu.
6 But whether we are in tribulation, [it is] for your encouragement and salvation, wrought in the endurance of the same sufferings which we also suffer,
Amma fa idan muna shan wuya, domin ta'aziyarku ne da cetonku. Haka kuma in mun ta'azantu, domin ta'aziyarku ne. Ta'aziyarku tana aiki ne sosai yayinda kuka jure da irin shan wuyar da mu ma muke sha.
7 (and our hope for you [is] sure; ) or whether we are encouraged, [it is] for your encouragement and salvation: knowing that as ye are partakers of the sufferings, so also of the encouragement.
Kuma gabagadinmu game da ku tabbatacce ne. Mun kuwa sani kamar yadda kuke tarayya cikin shan wahalhalun, haka kuma za ku yi tarayya cikin ta'aziyyar.
8 For we do not wish you to be ignorant, brethren, as to our tribulation which happened [to us] in Asia, that we were excessively pressed beyond [our] power, so as to despair even of living.
Gama ba mu so ku rasa sani, 'yan'uwa, game da tsananin da ya same mu a Asiya. An murkushe mu gaba daya har fiye da karfin mu, har ma mun fidda zuciya za mu rayu.
9 But we ourselves had the sentence of death in ourselves, that we should not have our trust in ourselves, but in God who raises the dead;
Hakika, mun ji hukuncin mutuwa akan mu. Amma wannan ya faru ne domin kada mu dogara ga kanmu, sai dai ga Allah, wanda ke tada matattu.
10 who has delivered us from so great a death, and does deliver; in whom we confide that he will also yet deliver;
Ya kubutar da mu daga wannan mummunan hatsari na mutuwa, kuma zai sake kubutar da mu. Mun kafa begenmu gare shi cewa zai sake kubutar da mu.
11 ye also labouring together by supplication for us that the gift towards us, through means of many persons, may be the subject of the thanksgiving of many for us.
Zai aikata wannan yayinda kuka taimake mu da addu'ar ku. Sa'an nan da dama za su bada godiya a madadin mu don tagomashin alheri da aka yi mana ta wurin addu'o'in mutane masu yawa.
12 For our boasting is this, the testimony of our conscience, that in simplicity and sincerity before God, (not in fleshly wisdom but in God's grace, ) we have had our conversation in the world, and more abundantly towards you.
Muna kuwa alfahari da haka: wato shaidar lamirinmu. Gama da kyakkyawan nufi da aminci da ke zuwa daga Allah muka tafiyar da rayuwarmu a Duniya. Mun yi wannan ne musamman tare da ku-ba kuwa cikin hikimar Duniya ba, amma ta wurin alherin Allah.
13 For we do not write other things to you but what ye well know and recognise; and I hope that ye will recognise to the end,
Bamu rubuta maku abinda ba za ku iya karantawa ko fahimta ba. Ina fata za ku fahimce mu baki daya,
14 even as also ye have recognised us in part, that we are your boast, even as ye [are] ours in the day of the Lord Jesus.
kamar yadda kuka fahimce mu kadan yanzu. Daganan a ranar Ubangijinmu Yesu za mu zama dalilinku na alfahari, kamar yadda za ku zama namu.
15 And with this confidence I purposed to come to you previously, that ye might have a second favour;
Saboda gabagadin da nake da shi game da haka, naso in zo gare ku da farko, domin ku amfana da ziyara sau biyu.
16 and to pass through to Macedonia by you, and again from Macedonia to come to you, and to be set forward by you to Judaea.
Ina da shirin ziyaratar ku a kan hanyata ta zuwa Makidoniya. Daga nan kuma ina da yi niyyar in sake ziyartar ku, a tafiya ta daga Makidoniya, domin ku aike ni a hanyata ta zuwa Yahudiya.
17 Having therefore this purpose, did I then use lightness? Or what I purpose, do I purpose according to flesh, that there should be with me yea yea, and nay nay?
Yayinda nake irin wannan tunani, ina shakka ne? Ina shirya abubuwa ne bisa ga magwajin mutum, ta yadda har zan ce “I, i” da “A, a, a, a” a lokaci guda?
18 Now God [is] faithful, that our word to you is not yea and nay.
Amma kamar yadda Allah yake amintacce, ba ma fadin ''I'' da ''A'a'' a lokaci guda.
19 For the Son of God, Jesus Christ, he who has been preached by us among you (by me and Silvanus and Timotheus), did not become yea and nay, but yea is in him.
Gama Dan Allah, Yesu Almasihu, wanda Silbanus da Sila, da Ni muka shaida maku, ba “I” da “A, a” ba ne. Maimakon haka, Shi “I” ne a kodayaushe.
20 For whatever promises of God [there are], in him is the yea, and in him the amen, for glory to God by us.
Gama dukan alkawaran Allah 'I' ne a cikin sa. Haka kuma ta wurin sa muna cewa ''Amin'' zuwa ga daukakar Allah.
21 Now he that establishes us with you in Christ, and has anointed us, [is] God,
Yanzu dai Allah ne ya tabbatar da mu da ku a cikin Almasihu, ya kuma kebe mu.
22 who also has sealed us, and given the earnest of the Spirit in our hearts.
Ya sa hatiminsa a kan mu ya kuma ba mu Ruhu a zuciyar mu a matsayin tabbacin abinda zai bamu daga baya.
23 But I call God to witness upon my soul that to spare you I have not yet come to Corinth.
Maimakon haka, na yi kira ga Allah ya zama shaida domina, cewa dalilin dayasa banzo Korintis ba domin in kare ku ne.
24 Not that we rule over your faith, but are fellow-workmen of your joy: for by faith ye stand.
Ba muna kokarin mu sarrafa yadda bangaskiyar ku za ta zama ba ne. Maimakon haka, muna aiki tare da ku ne domin farincikinku, yayinda kuke tsaye cikin bangaskiyarku.