< 2 Chronicles 32 >
1 After these things and this faithfulness, Sennacherib king of Assyria came and entered into Judah, and encamped against the fortified cities, and thought to break into them.
Bayan dukan abin da Hezekiya ya yi cikin aminci, sai Sennakerib sarkin Assuriya ya zo ya yaƙi Yahuda. Ya yi kwanto wa biranen katanga, yana zato zai ci su da yaƙi wa kansa.
2 And when Hezekiah saw that Sennacherib was come, and that he was minded to fight against Jerusalem,
Sa’ad da Hezekiya ya ga Sennakerib ya zo yana kuma niyya yă yaƙi Urushalima,
3 he took counsel with his princes and his mighty men to stop the fountains of waters that were outside the city; and they helped him.
sai ya yi shawara da fadawansa da hafsoshin mayaƙansa cewa su datse ruwa daga maɓulɓulan ruwan da yake waje da birnin, suka kuwa taimake shi.
4 And there was gathered together much people, and they stopped all the fountains, and the torrent that flows through the midst of the land, saying, Why should the kings of Assyria come and find much water?
Sai babban taro suka haɗu suka datse dukan maɓulɓulai da rafuffukan da suke gudu cikin ƙasar. Suka ce “Me zai sa sarakunan Assuriya su zo su sami ruwa barkatai?”
5 And he strengthened himself, and built up all the wall that was broken down, and raised it up to the towers, and [built] another wall outside, and fortified the Millo of the city of David, and made darts and shields in abundance.
Sai suka yi aiki tuƙuru suna gyaran dukan sassan katangar da suka fāɗi, suna kuma gina hasumiya a kai. Ya gina wata katanga a waje da wannan, ya kuma ƙara ƙarfin madogaran gini na Birnin Dawuda. Ya yi makamai masu yawa da kuma garkuwoyi.
6 And he set captains of war over the people, and assembled them to him on the open place at the gate of the city, and spoke consolingly to them saying,
Ya naɗa manyan hafsoshi a kan mutane, ya tattara su a gabansa a fili a ƙofar birni, ya kuma ƙarfafa su da waɗannan kalmomi.
7 Be strong and courageous, be not afraid nor dismayed for the king of Assyria, nor for all the multitude that is with him; for there are more with us than with him:
“Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro ko ku yi fargaba saboda sarkin Assuriya, da mayaƙan nan masu yawa da suke tare da shi, gama shi wanda yake tare da mu, ya fi wanda yake tare da su.
8 with him is an arm of flesh, but with us is Jehovah our God to help us and to fight our battles. And the people depended upon the words of Hezekiah king of Judah.
Mayaƙa na jiki ne kawai suke tare da shi, amma Ubangiji Allahnmu ne yake tare da mu, zai kuwa taimake mu yă kuma yi yaƙinmu.” Mutane kuwa suka amince da maganar Hezekiya, Sarkin Yahuda.
9 After this, Sennacherib king of Assyria sent his servants to Jerusalem (but he himself was before Lachish, and all his power with him), unto Hezekiah king of Judah, and unto all Judah that were at Jerusalem, saying,
Daga baya, sa’ad da Sennakerib sarkin Assuriya da dukan mayaƙansa suke kwanto wa Lakish, sai ya aiki hafsoshinsa da wannan saƙo wa Hezekiya sarkin Yahuda da kuma wa dukan mutanen Yahuda waɗanda suke can cewa,
10 Thus says Sennacherib king of Assyria: On what do ye rely that ye abide in the siege in Jerusalem?
“Ga abin da Sennakerib sarkin Assuriya ya ce ga me kake dogara, har da ka dāge cikin Urushalima da aka yi mata kwanto?
11 Does not Hezekiah persuade you, to give yourselves over to die by famine and by thirst, saying, Jehovah our God will deliver us out of the hand of the king of Assyria?
Ai, Hezekiya, ruɗinku yake yi, don yă sa ku mutu da yunwa da ƙishirwa sa’ad da yake ce muku, ‘Ubangiji Allahnmu zai cece mu daga hannun sarkin Assuriya.’
12 Has not the same Hezekiah removed his high places and his altars, and commanded Judah and Jerusalem saying, Ye shall worship before one altar, and burn incense upon it?
Hezekiya kansa bai rushe waɗannan masujadan kan tudu da bagadai, yana ce wa Yahuda da Urushalima, ‘Dole ku yi sujada a gaban bagade guda ku kuma ƙone hadayu a kansa ba’?
13 Do ye not know what I and my fathers have done to all the peoples of the countries? Were the gods of the nations of the countries in any wise able to deliver their country out of my hand?
“Ba ku san abin da ni da kuma kakannina suka yi wa dukan mutanen sauran ƙasashe ba? Allolin ƙasashen nan sun taɓa iya ceton ƙasarsu daga hannuna ne?
14 Who is there among all the gods of those nations that my fathers have utterly destroyed, that was able to deliver his people out of my hand, that your God should be able to deliver you out of my hand?
Wanne a cikin dukan allolin waɗannan ƙasashe da kakannina suka hallaka ya taɓa iya ceton mutanensa daga gare ni? To, yaya Allahnku zai iya cetonku daga hannuna?
15 And now, let not Hezekiah deceive you, nor persuade you in this manner, neither yet believe him; for no god of any nation or kingdom was able to deliver his people out of my hand, nor out of the hand of my fathers: how much less shall your God deliver you out of my hand?
Yanzu fa, kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku yă kuma ɓad da ku haka. Kada ku gaskata shi, gama babu allahn wata ƙasa ko masarautar da ya taɓa iya ceton mutanensa daga hannuna ko kuwa hannun kakannina. Balle har Allahnku yă cece ku daga hannuna!”
16 And his servants spoke yet more against Jehovah, the [true] God, and against his servant Hezekiah.
Hafsoshin Sennakerib suka ci gaba da maganar banza wa Ubangiji Allah da kuma a kan bawansa Hezekiya.
17 And he wrote a letter to rail at Jehovah the God of Israel, and to speak against him saying, As the gods of the nations of the countries have not delivered their people out of my hand, so shall not the God of Hezekiah deliver his people out of my hand.
Sarki ya kuma rubuta wasiƙu yana zagin Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana faɗin wannan a kansa, “Kamar yadda sauran allolin mutanen sauran ƙasashe ba su iya kuɓutar da mutane daga hannuna ba, haka Allahn Hezekiya ba zai kuɓutar da mutanensa daga hannuna ba.”
18 And they cried with a loud voice in the Jewish [language] to the people of Jerusalem that were on the wall, to frighten them and to trouble them; that they might take the city.
Sa’an nan suka yi magana da ƙarfi cikin Yahudanci wa mutanen Urushalima waɗanda suke kan katanga, don su firgita su, su kuma sa su ji tsoro don su iya cin birnin.
19 And they spoke of the God of Jerusalem as of the gods of the peoples of the earth, the work of man's hand.
Suka yi magana game da Allah na Urushalima yadda suka yi game da allolin sauran mutanen duniya, aikin hannuwan mutane.
20 And because of this, king Hezekiah and the prophet Isaiah the son of Amoz prayed and cried to heaven.
Sarki Hezekiya da annabi Ishaya ɗan Amoz suka yi kuka cikin addu’a ga sama game da wannan.
21 And Jehovah sent an angel, who cut off all the mighty men of valour, and the princes and the captains in the camp of the king of Assyria. And he returned with shame of face to his own land. And when he was come into the house of his god, they that came forth of his own bowels made him fall there with the sword.
Sai Ubangiji ya aiki mala’ika, wanda ya karkashe dukan jarumawa da shugabanni da kuma hafsoshi a sansanin sarkin Assuriyawa. Saboda haka sai sarkin Assuriya ya janye zuwa ƙasarsa da kunya. Da ya shiga haikalin Allahnsa, sai waɗansu a cikin’ya’yansa maza suka yanka shi da takobi.
22 And Jehovah saved Hezekiah and the inhabitants of Jerusalem from the hand of Sennacherib the king of Assyria, and from the hand of all, and protected them on every side.
Ta haka Ubangiji ya ceci Hezekiya da mutanen Urushalima daga hannun Sennakerib sarkin Assuriya da kuma daga hannun dukan sauran. Ya magance su a kowane gefe.
23 And many brought gifts unto Jehovah to Jerusalem, and precious things to Hezekiah king of Judah; and he was thenceforth magnified in the sight of all the nations.
Yawanci mutane suka kawo hadayun ƙonawa zuwa Urushalima wa Ubangiji da kuma kyautai masu daraja wa Hezekiya sarkin Yahuda. Daga lokacin zuwa gaba dukan ƙasashe suka girmama shi.
24 In those days Hezekiah was sick unto death, and he prayed to Jehovah; and he spoke to him and gave him a sign.
A kwanakin nan Hezekiya ya yi ciwo, ya yi kusan mutuwa. Sai ya yi addu’a ga Ubangiji, wanda ya amsa masa ya kuma ba shi alama.
25 But Hezekiah rendered not again according to the benefit [done] to him, for his heart was lifted up; and there was wrath upon him, and upon Judah and Jerusalem.
Amma zuciyar Hezekiya ta yi girman kai, bai kuwa yi amfani da alherin da aka nuna masa ba, saboda haka fushin Ubangiji ya sauko a kansa da kuma a kan Yahuda da Urushalima.
26 And Hezekiah humbled himself for the pride of his heart, he and the inhabitants of Jerusalem, so that the wrath of Jehovah came not upon them in the days of Hezekiah.
Sai Hezekiya ya tuba daga girma kan zuciyarsa, haka ma mutanen Urushalima; saboda haka fushin Ubangiji bai zo a kansu a kwanakin Hezekiya ba.
27 And Hezekiah had very much riches and honour; and he made himself treasuries for silver, and for gold, and for precious stones, and for spices, and for shields, and for all manner of pleasant vessels;
Hezekiya mai arziki da girma ne ƙwarai, ya kuma yi baitulmali domin azurfa da zinariyarsa da kuma domin duwatsu masu daraja, kayan yaji, garkuwoyi da kuma domin dukan kayayyaki masu daraja nasa.
28 storehouses also for the increase of corn and new wine and oil, and stalls for all manner of beasts, and [he procured] flocks for the stalls.
Ya kuma yi gine-gine domin ajiyar hatsi, sabon ruwa inabi da mai; ya kuma yi wuraren ajiyar kowane irin shanu dabam-dabam, da kuma turke domin tumaki.
29 And he provided for himself cities, and possessions of flocks and herds in abundance; for God gave him very much substance.
Ya gina ƙauyuka ya kuma samo shanu da garkuna masu yawa, gama Allah ya ba shi arziki mai yawa sosai.
30 And he, Hezekiah, stopped the upper outlet of the waters of Gihon, and brought it straight down to the west side of the city of David. And Hezekiah prospered in all his works.
Hezekiya ne ya datse ruwan bisa na maɓulɓular Gihon, ya sa ruwan ya gangara zuwa gefe yamma na Birnin Dawuda. Ya yi nasara a kome da ya yi.
31 However in [the matter of] the ambassadors of the princes of Babylon, who sent to him to inquire of the wonder that was done in the land, God left him, to try him, that he might know all [that was] in his heart.
Amma da masu mulkin Babilon suka aika da jakadu su tambaye shi game alamar da ta faru a ƙasar, Allah ya rabu da shi don yă gwada shi don yă kuma san kome da yake cikin zuciyarsa.
32 And the rest of the acts of Hezekiah and his good deeds, behold, they are written in the vision of the prophet Isaiah the son of Amoz in the book of the kings of Judah and Israel.
Sauran ayyukan mulkin Hezekiya da kuma kyawawa ayyukansa, suna a rubuce a cikin wahayin annabi Ishaya ɗan Amoz, a cikin littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
33 And Hezekiah slept with his fathers, and they buried him in the highest place of the sepulchres of the sons of David; and all Judah and the inhabitants of Jerusalem did him honour at his death. And Manasseh his son reigned in his stead.
Hezekiya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a kan tudu inda makabartan zuriyar Dawuda suke. Dukan Yahuda da kuma mutanen Urushalima suka girmama shi sa’ad da ya mutu. Sai Manasse ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.