< 1 Thessalonians 4 >
1 For the rest, then, brethren, we beg you and exhort you in [the] Lord Jesus, even as ye have received from us how ye ought to walk and please God, even as ye also do walk, that ye would abound still more.
A ƙarshe,’yan’uwa, mun umarce ku yadda za ku yi rayuwa domin ku gamshi Allah, kamar yadda kuke yi. Yanzu muna roƙonku muna kuma gargaɗe ku a cikin Ubangiji Yesu ku yi haka sau da sau.
2 For ye know what charges we gave you through the Lord Jesus.
Gama kun san umarnan da muka ba ku ta wurin ikon Ubangiji Yesu.
3 For this is [the] will of God, [even] your sanctification, that ye should abstain from fornication;
Nufin Allah ne a tsarkake ku, cewa ku guje wa fasikanci;
4 that each of you know how to possess his own vessel in sanctification and honour,
don kowannenku yă koya yadda zai ƙame kansa a hanyar da take mai tsarki, mai mutunci kuma,
5 (not in passionate desire, even as the nations who know not God, )
ba cikin muguwar sha’awa kamar ta marasa bangaskiya, waɗanda ba su san Allah ba;
6 not overstepping the rights of and wronging his brother in the matter, because the Lord [is] the avenger of all these things, even as we also told you before, and have fully testified.
cikin wannan al’amari kuwa kada wani yă yi wa ɗan’uwansa laifi ko yă cuce shi. Ubangiji zai hukunta mutane saboda dukan irin waɗannan zunubai, kamar yadda muka riga muka gaya muku, muka kuma yi muku gargaɗi.
7 For God has not called us to uncleanness, but in sanctification.
Gama Allah bai kira mu ga zaman marasa tsarki ba, sai dai ga zaman tsarki.
8 He therefore that [in this] disregards [his brother], disregards, not man, but God, who has given also his Holy Spirit to you.
Saboda haka, duk wanda ya ƙi wannan umarni ba mutum ne ya ƙi ba sai ko Allah, wanda ya ba ku Ruhunsa Mai Tsarki.
9 Now concerning brotherly love ye have no need that we should write to you, for ye yourselves are taught of God to love one another.
Yanzu kuwa game da ƙaunar’yan’uwa, ba ma bukata mu rubuta muku, gama ku kanku Allah ya riga ya koya muku ku ƙaunaci juna.
10 For also ye do this towards all the brethren in the whole of Macedonia; but we exhort you, brethren, to abound still more,
Gaskiyar kuwa ita ce, kuna ƙaunar dukan’yan’uwa ko’ina a Makidoniya. Duk da haka muna ƙara gargaɗe ku,’yan’uwa, ku yi haka sau da sau.
11 and to seek earnestly to be quiet and mind your own affairs, and work with your [own] hands, even as we charged you,
Ku mai da wannan burinku na yi natsattsiyar rayuwa, kuna mai da hankali ga sha’anin da yake gabanku, kuna kuma yin aiki da hannuwanku, kamar dai yadda muka gaya muku,
12 that ye may walk reputably towards those without, and may have need of no one.
don rayuwanku ta kullum ta zama da mutunci ga waɗanda suke na waje don kuma kada ku dogara a kan kowa.
13 But we do not wish you to be ignorant, brethren, concerning them that are fallen asleep, to the end that ye be not grieved even as also the rest who have no hope.
’Yan’uwa, ba ma so ku kasance cikin jahilci game da waɗanda suka yi barci, ko kuwa ku yi baƙin ciki kamar sauran mutanen da ba su da bege.
14 For if we believe that Jesus has died and has risen again, so also God will bring with him those who have fallen asleep through Jesus.
Mun gaskata cewa Yesu ya mutu ya tashi kuma daga matattu, ta haka muka gaskata cewa Allah zai kawo waɗanda suka yi barci a cikinsa tare da Yesu.
15 (For this we say to you in [the] word of [the] Lord, that we, the living, who remain to the coming of the Lord, are in no way to anticipate those who have fallen asleep;
Bisa ga maganar Ubangiji kansa, muna gaya muku cewa mu da muke raye har yanzu, waɗanda aka bari har dawowar Ubangiji, tabbatacce ba za mu riga waɗanda suka yi barci tashi ba.
16 for the Lord himself, with an assembling shout, with archangel's voice and with trump of God, shall descend from heaven; and the dead in Christ shall rise first;
Gama Ubangiji kansa zai sauko daga sama, da umarni mai ƙarfi, da muryar babban mala’ika da kuma busar ƙahon Allah, waɗanda suka mutu kuwa cikin Kiristi za su tashi da farko.
17 then we, the living who remain, shall be caught up together with them in [the] clouds, to meet the Lord in [the] air; and thus we shall be always with [the] Lord.
Bayan haka, mu da muke da rai da aka bari, za a ɗauke mu tare da su a cikin gizagizai don mu sadu da Ubangiji a sararin sama. Ta haka za mu kasance tare da Ubangiji har abada.
18 So encourage one another with these words.)
Saboda haka ku ƙarfafa juna da waɗannan kalmomi.