< 1 John 1 >
1 That which was from [the] beginning, that which we have heard, which we have seen with our eyes; that which we contemplated, and our hands handled, concerning the word of life;
Abin nan da yake tun daga farko, wanda muka ji, wanda muka gani da idanunmu, wanda muka gani hannuwanmu suka kama, a wajen maganar rai.
2 (and the life has been manifested, and we have seen, and bear witness, and report to you the eternal life, which was with the Father, and has been manifested to us: ) (aiōnios )
Ran kuwa aka baiyyana shi, muka gani, muka bada shaida, muka gaya maku labarin rai na har abada, wanda da yake a wurin Uba, aka kuma sanar da mu. (aiōnios )
3 that which we have seen and heard we report to you, that ye also may have fellowship with us; and our fellowship [is] indeed with the Father, and with his Son Jesus Christ.
Wannan da muka gani muka ji muka baku labari, domin kuyi zumunci da mu, zumuncinmu kuwa tare da Uba yake da Dansa Yesu Almasihu.
4 And these things write we to you that your joy may be full.
Haka nan, muna rubuta maku wadannan abubuwa domin farin cikinmu ya cika.
5 And this is the message which we have heard from him, and declare to you, that God is light, and in him is no darkness at all.
Wannan shi ne sakon da muka ji daga wurinsa mu kuwa muka sanar da ku: Allah haske ne a wurinsa kuwa babu duhu ko kadan.
6 If we say that we have fellowship with him, and walk in darkness, we lie, and do not practise the truth.
Idan mun ce muna zumunci da shi kuma muna tafiya cikin duhu, muna yin karya kuma bama aikata gaskiya.
7 But if we walk in the light as he is in the light, we have fellowship with one another, and the blood of Jesus Christ his Son cleanses us from all sin.
Amma idan muna tafiya cikin haske kamar yadda yake cikin haske, muna zumunci da juna, jinin Yesu Dansa ya wankemu daga dukka zunubi.
8 If we say that we have no sin, we deceive ourselves, and the truth is not in us.
Idan mun ce bamu da zunubi, muna rudin kanmu kenan, ba kuma gaskiya a cikinmu.
9 If we confess our sins, he is faithful and righteous to forgive us [our] sins, and cleanse us from all unrighteousness.
Amma idan mun fadi zunubanmu, shi mai aminci ne, mai adalci da zai gafarta mana zunubanmu, ya kuma wankemu daga dukkan rashin adalci.
10 If we say that we have not sinned, we make him a liar, and his word is not in us.
Idan mun ce bamu yi zunubi ba, mun mai da shi makaryaci kenan, maganarsa kuma bata cikinmu.