< 1 Corinthians 11 >
1 Be my imitators, even as I also [am] of Christ.
Ku bi gurbina, kamar yadda ni nake bin gurbin Kiristi.
2 Now I praise you, that in all things ye are mindful of me; and that as I have directed you, ye keep the directions.
Ina yabonku saboda kuna tunawa da ni a cikin kowane abu, kuna kuma riƙe da koyarwar, yadda na ba ku.
3 But I wish you to know that the Christ is the head of every man, but woman's head [is] the man, and the Christ's head God.
To, ina so ku gane cewa shugaban kowane namiji Kiristi ne, shugaban mace namiji ne, shugaban Kiristi kuma Allah ne.
4 Every man praying or prophesying, having [anything] on his head, puts his head to shame.
Kowane namijin da ya yi addu’a ko annabci da kansa a rufe ya jawo kunya wa kansa.
5 But every woman praying or prophesying with her head uncovered puts her own head to shame; for it is one and the same as a shaved [woman].
Duk macen da ta yi addu’a ko annabci da kanta a buɗe kuwa ta rena kanta, ya zama kamar an aske kanta ke nan.
6 For if a woman be not covered, let her hair also be cut off. But if [it be] shameful to a woman to have her hair cut off or to be shaved, let her be covered.
In mace ba ta so tă rufe kanta, to, sai tă aske gashinta; in kuwa abin kunya ne mace tă yanke ko tă aske gashinta, to, sai tă rufe kanta.
7 For man indeed ought not to have his head covered, being God's image and glory; but woman is man's glory.
Namiji kuwa bai kamata ya rufe kansa ba, da yake shi kamannin Allah ne, da kuma darajar Allah, amma mace dai, darajar namiji ne.
8 For man is not of woman, but woman of man.
Gama namiji bai fito daga mace ba, sai dai mace ce ta fito daga namiji.
9 For also man was not created for the sake of the woman, but woman for the sake of the man.
Ba a kuma halicci namiji don mace ba, sai dai mace don namiji.
10 Therefore ought the woman to have authority on her head, on account of the angels.
Don haka, saboda wannan, da kuma saboda mala’iku, dole mace ta ɗaura wani abu a kanta.
11 However, neither [is] woman without man, nor man without woman, in [the] Lord.
Duk da haka a cikin Ubangiji, mace ba a rabe take da namiji ba, namiji kuma ba a rabe yake da mace ba.
12 For as the woman [is] of the man, so also [is] the man by the woman, but all things of God.
Kamar yadda mace ta fito daga namiji, haka kuma aka haifi namiji ta wurin mace. Sai dai kowane abu daga Allah yake.
13 Judge in yourselves: is it comely that a woman should pray to God uncovered?
Ku kanku duba mana. Ya yi kyau mace tă yi addu’a ga Allah da kanta a buɗe?
14 Does not even nature itself teach you, that man, if he have long hair, it is a dishonour to him?
Kai, yadda halitta take ma, ai, ta koya muku cewa in namiji yana da dogon gashi, abin kunya ne a gare shi,
15 But woman, if she have long hair, [it is] glory to her; for the long hair is given [to her] in lieu of a veil.
amma in mace tana da dogon gashi, ai, daraja ce a gare ta. Gama an ba ta dogon gashi saboda rufe kanta ne.
16 But if any one think to be contentious, we have no such custom, nor the assemblies of God.
In akwai mai gardama da wannan, to, mu dai ba mu da wata al’ada, haka ma ikkilisiyoyin Allah.
17 But [in] prescribing [to you on] this [which I now enter on], I do not praise, [namely, ] that ye come together, not for the better, but for the worse.
Game da umarnan nan dai, ban yaba muku ba, domin taruwarku ba ta kirki ba ce, ɓarna ce.
18 For first, when ye come together in assembly, I hear there exist divisions among you, and I partly give credit [to it].
Da farko dai, na ji cewa sa’ad da kuka taru a matsayin ikkilisiya, akwai tsattsaguwa a tsakaninku, har na fara yarda da zancen.
19 For there must also be sects among you, that the approved may become manifest among you.
Ba shakka dole a sami bambanci a tsakaninku don a nuna wa Allah ya amince da shi a cikinku.
20 When ye come therefore together into one place, it is not to eat [the] Lord's supper.
Sa’ad da kuka taru, ba Cimar Ubangiji kuke ci ba,
21 For each one in eating takes his own supper before [others], and one is hungry and another drinks to excess.
gama yayinda kuke ci, kowa yakan ci gaba ba tare da jiran wani ba. Wani yă zauna da yunwa, wani kuma yă bugu.
22 Have ye not then houses for eating and drinking? or do ye despise the assembly of God, and put to shame them who have not? What shall I say to you? shall I praise you? In this [point] I do not praise.
Kai, ba ku da gidajen da za ku ci ku sha ne? Ko dai kun rena ikkilisiyar Allah ne, kuna kuma wulaƙanta waɗanda ba su da kome? Me zan ce muku? In yabe ku ne game da wannan? A’a, ko kaɗan!
23 For I received from the Lord, that which I also delivered to you, that the Lord Jesus, in the night in which he was delivered up, took bread,
Gama abin da na karɓa daga wurin Ubangiji shi ne nake ba ku. Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi, ya ɗauki burodi,
24 and having given thanks broke [it], and said, This is my body, which [is] for you: this do in remembrance of me.
bayan ya yi godiya, sai ya kakkarya ya ce, “Wannan jikina ne, wanda yake dominku, ku yi wannan don tunawa da ni.”
25 In like manner also the cup, after having supped, saying, This cup is the new covenant in my blood: this do, as often as ye shall drink [it], in remembrance of me.
Haka kuma bayan cimar, ya ɗauki kwaf, yana cewa, “Wannan kwaf ne sabon alkawari a jinina; ku yi wannan, a duk sa’ad da kuke sha, don tunawa da ni.”
26 For as often as ye shall eat this bread, and drink the cup, ye announce the death of the Lord, until he come.
Gama a duk sa’ad da kuke cin wannan burodi, kuke kuma sha daga wannan kwaf, kuna shelar mutuwar Ubangiji ne har yă dawo.
27 So that whosoever shall eat the bread, or drink the cup of the Lord, unworthily, shall be guilty in respect of the body and of the blood of the Lord.
Saboda haka, duk wanda ya ci burodin ko ya sha daga kwaf na Ubangiji da rashin cancanta, ya yi laifin wulaƙanta jiki da jinin Ubangiji ke nan.
28 But let a man prove himself, and thus eat of the bread, and drink of the cup.
Dole kowa yă bincike kansa kafin yă ci burodin yă kuma sha daga kwaf ɗin.
29 For [the] eater and drinker eats and drinks judgment to himself, not distinguishing the body.
Gama duk wanda ya ci ya kuma sha ba tare da fahimtar jikin Ubangiji ba, ya ci ya kuma sha wa kansa hukunci ne.
30 On this account many among you [are] weak and infirm, and a good many are fallen asleep.
Shi ya sa da yawa a cikinku ba su da ƙarfi, suna kuma da rashin lafiya, waɗansunku kuma sun riga sun yi barci.
31 But if we judged ourselves, so were we not judged.
Amma in da za mu auna kanmu sosai, da ba za mu shiga irin hukuncin nan ba.
32 But being judged, we are disciplined of [the] Lord, that we may not be condemned with the world.
Duk da haka sa’ad da Ubangiji ya hukunta mu, ana yin mana horo ne don kada a ƙarshe a hallaka mu tare da duniya.
33 So that, my brethren, when ye come together to eat, wait for one another.
Saboda haka’yan’uwana, sa’ad da kuka taru don ci, ku jira juna.
34 If any one be hungry, let him eat at home, that ye may not come together for judgment. But the other things, whenever I come, I will set in order.
In wani yana jin yunwa, sai yă ci abinci a gida, saboda in kuka taru kada yă jawo hukunci. Sa’ad da na zo kuma zan ba da ƙarin umarnai.