< 1 Chronicles 20 >
1 And it came to pass at the time of the return of the year, at the time when kings go forth, that Joab led forth the power of the army, and laid waste the land of the children of Ammon, and came and besieged Rabbah. But David abode at Jerusalem. And Joab smote Rabbah, and overthrew it.
Da bazara, a lokacin da sarakuna kan tafi yaƙi, Yowab ya jagorance mayaƙa. Ya lalatar da ƙasar Ammonawa ya kuma tafi Rabba ya yi mata kwanto, amma Dawuda ya zauna a Urushalima. Yowab ya yaƙi Rabba, ya kuma bar ta kango.
2 And David took the crown of their king from off his head, and found it to weigh a talent of gold, and there were precious stones in it; and it was [set] upon David's head: and he brought forth the spoil of the city in great abundance.
Dawuda ya ɗauki rawani daga kan sarkinsu, nauyinsa ya kai talenti na zinariya, aka kuma yi masa ado da duwatsu masu daraja, sai Dawuda kuwa ya sa a kansa. Ya kuma kwashi ganima mai yawa daga birnin
3 And he brought out the people that were in it, and cut them with the saw, and with harrows of iron, and with saws. And so David did to all the cities of the children of Ammon. And David and all the people returned to Jerusalem.
ya kuma fitar da mutanen da suke can, ya sa su aiki da zartuna da makamai masu kaifi da kuma gatura. Dawuda ya yi haka da dukan garuruwan Ammonawa. Sa’an nan Dawuda da mayaƙansa gaba ɗaya suka koma Urushalima.
4 And it came to pass after this, that there arose war at Gezer with the Philistines; then Sibbechai the Hushathite smote Sippai, one of the children of Rapha; and they were subdued.
Ana nan, sai yaƙi ya ɓarke a Gezer tsakanin Isra’ila da Filistiyawa. Sai Sibbekai mutumin Husha ya kashe Siffai, ɗaya daga cikin zuriyar Refahiyawa, ta haka kuma aka ci Filistiyawa da yaƙi.
5 And there was again a battle with the Philistines; and Elhanan the son of Jair smote Lahmi the brother of Goliath the Gittite; now the shaft of his spear was like a weaver's beam.
Yaƙi kuma ya sāke tashi tsakanin Isra’ilawa da Filistiyawa, Elhanan ɗan Yayir ya kashe Lahmi ɗan’uwan Goliyat mutumin Gat, wanda yake riƙe da māshi mai sandan masaƙa.
6 And there was again a battle, at Gath; and there was a man [there] of great stature, whose fingers [and toes] were four and twenty, six [on each hand], and six [on each foot]; and he also was born to Rapha.
Aka sāke yin wani yaƙin kuma, wanda ya faru a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu da kuma yatsotsi shida a kowace ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriyar Rafa ce.
7 And he defied Israel; but Jonathan the son of Shimea David's brother smote him.
Sa’ad da ya yi wa Isra’ila ba’a, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwan Dawuda ya kashe shi.
8 These were born to Rapha in Gath; and they fell by the hand of David, and by the hand of his servants.
Waɗannan su ne zuriyar Rafa a Gat, Dawuda da mutanensa sun kashe su.